Shugaban hukumar zaɓe mai zaman kanta (INEC) na ƙasa, Farfesa Mahmud Yakubu na shan suka kan ayyana Bola Tinubu a matsayin wanda ya lashe zaɓen 2023.
Wannan suka da ake wa Yakubu na zuwa ne yayin da ƴan Najeriya ke fama da wahalhalun rayuwa da yunwa waɗanda ake ganin gwamnatin Tinubu ce ta kawo su.
yanzu kuma an fara yaɗa ikirarin cewa shugaban INEC ya fitar da wata sanarwa, wanda ta nuna nadamar ayyana Bola Tinubu a matsayin wanda ya samu nasara a zaɓen.
A sanarwan, an ce Yakubu ya ce ya yi da na-sanin gaggauta ba Tinubu nasara bayan ganin halin ƙuncin rayuwar da aka shiga a ƙasar nan.
Mafi yawan ƴan Najeriya a manhajar X suna ganin laifin shugaban INEC a wannan halin wahala da aka shiga karkashin mulkin Tinubu tun kafin ya cika shekara ɗaya.
A wani rahoto da Igbo Times Magazine ta wallafa, ya ce: ” Na yi saurin ayyana Tinubu a matsayin shugaban ƙasa, ban taɓa tsammanin ƴan Najeriya za su shiga wahala ba – Shugaban INEC.
Shugaban INEC ya bayyana nadamar saurin ayyana Tinubu a matsayin shugaban Najeriya bayan ganin wahalar da mutane ke ciki.
“Shugaban hukumar zaɓe INEC ya fitar da sanarwa mai nuna nadamar da ya yi da bayyana Bola Tinubu a matsayin shugaban ƙasa a Najeriya.”












