Tsohon gwamnan jihar Jigawa, Sule Lamido, ya yi watsi da ikirarin da ake na cewa yana shirin shiga jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) gamayyar jam’iyyar, yana mai jaddada cewa ya ci gaba da kasancewa a jam’iyyar Peoples Democratic Party (PDP domin haryanzu babu wani tsarin daya gamsu dashi a jam’iyyar ADC.
Da yake magana yayin tattaunawa da manema labarai a Kano ranar Talata, Lamido ya amince da kalubalen da jam’iyyar adawa ta PDP ke fuskanta a halin yanzu sai dai ya jaddada cewa shi ne mutum na karshe da zai shiga kawancen ADC.
Ya yi jawabi ne kan jita-jitar da ke nuna kasancewar sa a jam’iyyar ADC da kuma zargin goyon bayan takarar Peter Obi a cikin jam’iyyar.
A cewar Lamido, kamata ya yi kawancen siyasa ya kasance mai tushe bisa ingantattun ka’idoji, hadin kai, kwanciyar hankali, tsaro, da ci gaban kasa, ba wai wani buri na kashin kai, ko daukar fansa, ko buri na gajeren lokaci ba.
Ya bayyana damuwarsa cewa manufar hadakar jam’iyyar ADC a halin yanzu ta shafi buri ne na kashin kai maimakon hada kai ga al’ummar kasar gabanin zaben 2027.
Lamido, mamba a kwamitin amintattu na jam’iyyar PDP (BoT), ya jaddada kudirinsa na goyon bayan duk wani ɗan takara daga cikin jam’iyyar PDP ko a wajensa, wanda ya mayar da hankali wajen dawo da martabar Nijeriya da ta rasa, da kuma kawar da jam’iyya mai mulki daga mulki a 2027.












