24/07/2026
Daga Khadija Muhammad Maitaya
Shugaban Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa INEC, Farfesa Joash Amupitan, ya tabbatar wa ‘yan kasar nan cewa ƙuri’unsu za su yi tasiri a babban zaɓen shekarar 2027.
Amupitan ya bayyana hakan ne a Juma’ar nan,yayin wata ziyarar girmamawa da ya kai wa tsohon Shugaban Ƙasa na Mulkin Soja kuma Shugaban Kwamitin Zaman Lafiya na Ƙasa, Janar Abdulsalami Abubakar mai ritaya a gidansa da ke Minna, a Jihar Neja.
Shugaban na INEC ya jagoranci tawagar da ta haɗa da Kwamishinonin Hukumar na Ƙasa da Sakataren Hukumar da daraktoci da masu ba shi shawara kan harkokin fasaha.
Amupitan ya bayyana Abdulsalami Abubakar a matsayin “uban dimokuraɗiyya a Najeriya,” yana mai cewa jagorancin da ya yi wajen miƙa mulki ga farar hula a shekarar 1999 ya zama wani muhimmin tarihi a tafiyar dimokuraɗiyyar ƙasar nan.
Ya ce hukumar INEC tana kallon tsohon shugaban ƙasar ba kawai a matsayin dattijon ƙasa ba, har ma a matsayin ginshiƙin goyon baya ga hukumar.
Haka kuma, ya yaba da rawar da Abdulsalami Abubakar ke takawa a matsayin Shugaban Kwamitin Zaman Lafiya na Ƙasa, yana mai cewa yarjejeniyar zaman lafiya da kwamitin ke shirya wa jam’iyyun siyasa tana da matuƙar tasiri wajen ƙarfafa ɗabi’a da zaman lafiya a tsarin siyasar kasar nan.










