• About
  • Advertise
  • Privacy & Policy
  • Contact
AKSAM
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO
No Result
View All Result
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO
No Result
View All Result
AKSAM
No Result
View All Result

Shugaban Hukumar Gudanarwar UBRBDA, Barayan Bauchi, Ya Yabawa Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu Kan Ware Naira Tiriliyan 1.2 Da Aka Saka Cikin Bankin Manoman Najeriya

aksam by aksam
August 23, 2025
Reading Time: 3 mins read
0
Home Uncategorized
ADVERTISEMENT
472
SHARES
1.5k
VIEWS
Share on FacebookShare on Twitter

 

 

RelatedPosts

Halifatul Akabar Sheikh Ahmad Abdullah Mai Kano Jallo Ya Halarci Mulundin Garin Zangon Nkawkawo

Irin Yadda Aka Gudanar Da Zagayen Mauludn Tunawa Ga Ranar Da Aka Haifi Annabi Muhammadu SWA A Garin Nkawkawo

Kasar Ghana Ta Bayyana Shirinta Na ƙara Samar Da Wutar Lantarki Domin Sayarwa Najeriya Da Sauran ƙasashen Yammacin Afirka

Daga: Hassan Umar Gwammaja

Shugaban Hukumar Gudanarwa na Hukumar Raya Kogin Benue ta Arewa (UBRBDA), wadda ke kula da Jahohin Adamawa, Bauchi, Gombe, da Taraba, Alhaji Sanusi Muhammad Baban Takko (Barayan Bauchi), ya yi yabon da kuma jinjinawa Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu (Jagaban Najeriya) saboda jajircewarsa da ƙwazon da ya nuna wajen farfado da Bankin Manoman Najeriya.

Yayin da yake bayani kan ci gaban, Barayan Bauchi ya bayyana amincewar Naira Tiriliyan 1.2 domin farfado da noman zamani, noman rani, da sauran tsare-tsaren noma a matsayin mataki mai matuƙar muhimmanci wanda zai maido da noma a matsayin ginshiƙin bunƙasar tattalin arzikin Najeriya, musamman Arewacin ƙasar, kamar yadda aka sani a da.

“A matsayina na Shugaban Hukumar Gudanarwa ta Upper Benue River Basin Development Authority, ina mika gaisuwa da goyon baya na gaskiya ga shugaban ƙasarmu mai ƙarfi da basira, Bola Ahmed Tinubu, GCFR, saboda wannan muhimmin mataki da bai taɓa faruwa ba a tarihin ƙasar. Amincewa da wannan babbar adadi na kuɗi zuwa Bankin Manoma na Najeriya domin bashi ga manoma na gaskiya, zai ƙarfafa ci gaban sashen noma, tabbatar da girbin amfanin gona mai yawa, ɗorewar abinci, fitar da kaya zuwa ƙasashen waje, da walwala ga al’umma, har ma da samar da dukiya domin amfanin dukkan ‘yan Najeriya,” in ji shi.

Sai dai Barayan Bauchi, ya roƙi shugabancin Bankin Manoma na Najeriya da su tabbatar da cewa sharuddan karɓar bashin ba su da wahala, yana mai jaddada cewa wannan shi ne kawai hanyar da za a iya cimma burin da muradin mai girma Shugaba Bola Ahmed Tinubu da tawagarsa na ganin Najeriya ta zama ɗaya daga cikin manyan ƙasashen da ke samar da abinci a Afirka, ƙasa da hamadar Sahara da ma duniya baki ɗaya.

Ya ƙara da cewa ƙasashe masu tasowa kamar India da Siri-Lanka sun aiwatar da irin wannan tsari da nasara mai yawa, inda ‘yan ƙasarsu suka more ruwan demokiradiyya ta hanyar wadataccen abinci da bunƙasar noma.

“A wannan dama, ina kiran cibiyoyin gargajiya da sauran masu ruwa da tsaki da su wayar da kan al’ummarmu a ƙarkara a faɗin ƙasa kan wannan sabon tsari na hukuma. Samuwar wadannan kuɗaɗe, Naira Tiriliyan 1.2, da aka saka a cikin Bankin Noma na Najeriya a matsayin bashin ju-yin-ju-ya hali,  na da nufin ba da numfashi ga sashen noma da ya kusa durƙushewa,” in ji Barayan Bauchi.

Shugaban Hukumar UBRBDA ya ƙara tabbatar da cewa, a ƙarƙashin jagorancinsa, hukumar za ta yi aiki kafada da kafada da Bankin Manoma na Najeriya domin ganin cewa Manoman, matasa da manoman rani a jihohin huɗu da ke ƙarƙashin UBRBDA sun ci gajiyar wannan shiri na sauyi da ya fito daga Agenda na Sabon Fata na Shugaba Bola Ahmed Tinubu.

Ya bayyana cewa wannan yana da matuƙar muhimmanci ganin irin matsalolin jinƙai da wannan yanki ya fuskanta sakamakon shekaru na rikice-rikice da sauran ƙalubale.

Har ila yau, Barayan Bauchi ya bukaci Bankin Manoma na Najeriya da ya buɗe ofisoshi a dukkan ƙananan hukumomi 774 na Najeriya, har da yankunan ƙananan hukumomin babban birnin tarayya (FCT), domin buɗe kofofin dama ga manoman gaskiya a ƙarkara, daidai da hangen nesa na shugaban ƙasa na aiki don amfanin kowa da kowa a kowane mataki.

Yayin da yake nuna matuƙar godiyarsa, Barayan Bauchi ya yabawa Shugaba Bola Ahmed Tinubu bisa jajircewarsa wajen gyara manyan sassa na tattalin arzikin ƙasa ta hanyar manyan sauye-sauye tun bayan da ya hau mulki kusan shekaru biyu da suka wuce.

“Mai Girma Shugaban Ƙasa, tarihi da al’umma za su tuna da kai da alheri saboda ƙaddamar da muhimman sauye-sauye da suka shafi magance matsalolin tsaro da abinci da sauran sassan rayuwa. Ina roƙonka da kada ka gaji ko ka karaya a wannan tafiya ta gina ƙasa da kuma gina ƙungiyoyin al’umma da adalci da dai-daito ga kowa da kowa. Kamar yadda ka faɗa, bayan duhu, safiya mai daraja tana zuwa,” in ji shi.

Share189Tweet118SendShare
ADVERTISEMENT
Previous Post

Invitation !!!

Next Post

Kwamitin Fadakar Da Al’umma Mahimmanci Mallakar Katin Zabe Ya Ziyarci Shugaban Hukumar Zabe Na Jihar Kano

aksam

aksam

RelatedPosts

Halifatul Akabar Sheikh Ahmad Abdullah Mai Kano Jallo Ya Halarci Mulundin Garin Zangon Nkawkawo
Uncategorized

Halifatul Akabar Sheikh Ahmad Abdullah Mai Kano Jallo Ya Halarci Mulundin Garin Zangon Nkawkawo

by aksam
September 5, 2026
Irin Yadda Aka Gudanar Da Zagayen Mauludn Tunawa Ga Ranar Da Aka Haifi  Annabi Muhammadu SWA  A Garin Nkawkawo
Uncategorized

Irin Yadda Aka Gudanar Da Zagayen Mauludn Tunawa Ga Ranar Da Aka Haifi Annabi Muhammadu SWA A Garin Nkawkawo

by aksam
September 1, 2026
Kasar Ghana Ta Bayyana Shirinta Na ƙara Samar Da Wutar Lantarki Domin Sayarwa Najeriya Da Sauran ƙasashen Yammacin Afirka
Uncategorized

Kasar Ghana Ta Bayyana Shirinta Na ƙara Samar Da Wutar Lantarki Domin Sayarwa Najeriya Da Sauran ƙasashen Yammacin Afirka

by aksam
August 26, 2026
Hukumar Kashe Gobara Ta Jihar Kano Ta Dakile Wata Gobara A Rano
Uncategorized

Hukumar Kashe Gobara Ta Jihar Kano Ta Dakile Wata Gobara A Rano

by aksam
August 26, 2026

Comments 0

  1. Engr. Maidabino Umar says:
    1 year ago

    Barayan Bauchi, Alhaji Sanusi Baban Takko Yayi Gaskiya.

    Dattijon Arziki Kuma Jagora Abin Kwaikwayo.

    Hakika Munji Dadin Wannan Labarin Kuma Shugaban Tarayyar Najeriya, Maigirma Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu, GCFR, Ya Cancanci Yabo. Itama Bankin Manoma na Najeriya Muna Fatan ZASUYI Abinda Yadace Wurin Ganin Al’umma Manoma Na Zahiri Sunci Gajiyar Wannan Kudaden Noma Batareda Tsauraran Sharuddaba

    Muna Godiya Matuka Alhaji Sanusi Baban Takko, Barayan Bauchi.

    Reply

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Recommended.

Neman saukin rayuwa, wani gwamna ya umarci Mutanen jihar sa su tashi da Azumi domin yin Addu’a ta musamman

Neman saukin rayuwa, wani gwamna ya umarci Mutanen jihar sa su tashi da Azumi domin yin Addu’a ta musamman

February 20, 2024
Abin Mamaki, Karon farko Najeriya ta ƙera jirgin yaƙi Maras Matuƙi

Abin Mamaki, Karon farko Najeriya ta ƙera jirgin yaƙi Maras Matuƙi

January 24, 2026
ADVERTISEMENT

Trending.

Masu Siye Da Siyar Da Filaye A  R/zakara Sunkoka Da Aibantasu Da Gwamnatin Kano Keyi.

Masu Siye Da Siyar Da Filaye A  R/zakara Sunkoka Da Aibantasu Da Gwamnatin Kano Keyi.

August 26, 2026
Cristiano Ronaldo Ya Auri Georgina Rodríguez

Cristiano Ronaldo Ya Auri Georgina Rodríguez

August 12, 2026
Wani Kauran Mata Ya Jikkata Wata Dattijuwa Bayan Ta Hana Shi Shiga Gurin Da Bai kamata Ba

Wani Kauran Mata Ya Jikkata Wata Dattijuwa Bayan Ta Hana Shi Shiga Gurin Da Bai kamata Ba

August 29, 2026
Iran Ta Kakkabo Wasu Manyan Jiragen Yaƙi Na Amurka

Iran Ta Kakkabo Wasu Manyan Jiragen Yaƙi Na Amurka

August 14, 2026
Masu Zuba Jari 40+ daga Masar na Sha’awar Zuba Jari A Najeriya

Masu Zuba Jari 40+ daga Masar na Sha’awar Zuba Jari A Najeriya

August 23, 2026

Aksam Hausa

AKSAM MEDIA is a company which designed as online News Platform and other activities related to develop society.

The AKSAM MEDIA created since November 2019 and it does many activities as News publishes it publishes a Hausa News And English News.

No Result
View All Result
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO

© 2023 Aksam media