Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, ya roƙi masu fatan alheri da su guji saka tallan taya shi murnar cikar shekaru 60 a jaridu, da kuma watsa saƙonnin taya murna ta gidajen rediyo, talabijin da kafafen sadarwa na zamani.
Shettima ya bayyana hakan ne ranar Asabar, cikin wata sanarwa da Babban Mataimaki na Musamman ga Shugaban Ƙasa kan Yaɗa Labarai da Sadarwa, Mista Stanley Nkwocha, ya fitar.
Ya ce shawarar da ya yanke na gudanar da bikin cikin sauƙi ta samo asali ne daga imaninsa cewa ya kamata hankalin jama’a ya kasance kan muhimman ayyukan raya ƙasa, maimakon shagulgulan bikin mutum na kansa.
Ya ce: “Domin tabbatar da cikakkiyar dacewa, ina roƙon kowa da kada a gudanar da wani bikin murnar zagayowar ranar haihuwa a bainar jama’a, tarukan taya murna ko tallan fatan alheri a kafafen yaɗa labarai na buga takardu, rediyo, talabijin da kafafen sadarwa na zamani.”










