Mai alfarma Sarkin Musulmi ya yi magana kan halin ƙunci da tsadar rayuwa da ƴan Najeriya suka tsinci kansu a ciki a wannan lokacin
Sarkin ya bayyana hakan ne a wajen gagarumin taron buɗe masallacin Juma’a da ƙungiyar Jama’atu Izalatil Bidi’a Wa’kamatis Sunnah (JIBWIS) ta gina a Guzape, Abuja.
Alhaji Sa’ad Abubakar III ya bayyana cewa kaucewa Allah da aka yi shi ne babban dalilin da ya sanya aka shiga cikin wannan halin
Sarkin Musulmin ya shawarci ƴan Najeriya da su tuba su koma ga Allah domin fita daga cikin wannan halin ƙuncin
”Duk wanda ya bar bautar Allah, to haƙiƙa Allah ba zai kalli ɓangarensa ba, hakan ya tabbata a wurare da dama a cikin Alkur’ani mai girma. Za mu ci gaba da ba gwamnati shawara ta gaskiya.”












