Gwamnan jihar Ekiti ya bayyana bukatar a kawo sauyi ga yadda ake amfani da kafafen sada zumunta musammam ma a Najeriya
Najeriya na daga kasashen da kowa ke fadin abin da ya ga dama a kafar sada zumunta ba tare da daukar mataki kan lokaci ba
Ya bayyana ta yadda hakan zai taimaka wajen kawo ci gaba da wanzuwar ababen alheri ga kasar mai dimbin matasa da ke amfani da yanar gizo
Gwamnan ya bayyana hakan ne a wani rubutun da ya yada a kafar Twitter, inda yace rashin hakan barazana ce babba ga Najeriya.
A cewar gwamnan, tabbas kafafen sada zumunta na da amfani, amma barin sakaka babu wata kula ka iya jefa kasar nan ga hadari nan gaba.
Ya ce, samar da ka’idojin zasu taimaka wajen tabbatar da amfani da kafafen ta hanyoyin da suka dace kwarai.
A kalamansa, gwamnan ya ce: “Gaskiyar da ya kamata mu fuskanta ita ce ba zai yiwu mu ci gaba da amfani da kafafen sada zumunta babu ka’ida ba. Dole ne a tsara ka’idojin amfani da shi daidai da doka ga masu dandamali da masu amfani dashi.
“Babu shakka kafofin sada zumunta sun zama masu mahimmanci ga wanzuwarmu, amma dole ne a sami ka’idojin da ke jagorantar amfani da shi.”












