Farfesa Farooq Kperogi, ya bukaci Shugaban kasa Bola Tinubu da ya kula da zanga-zangar da ake yi kan tsadar rayuwa
A wani rubutu da ya wallafa, Farfesa Kperogi ya ce idan ba a magance lamarin ba, za a gudanar da zanga-zanga a fadin kasar nan da ‘dan lokaci
Jaridar Legit ta ruwaito cewa Kperogi ya bukaci Shugaban kasa Tinubu da ya daina yin abubuwa kamar magabacinsa, Muhammadu
A rubutunsa da ya yi na mako, Kperogi ya yi gargadin cewa idan har manufofinsa (Tinubu) na rashin tausayi ya haifar da bore na gama gari, yankin Kudu maso Yamma ba zai zame masa kariya ba.
Marubucin ya bayyana cewa mafita guda akan abin da ya bayyana a matsayin ‘hatsari’ shine Shugaban kasa Tinubu ya yi shugabanci nagari da tausayi.
Kperogi ya rubuta: “Sakin dubban Metric Tan na hatsi mataki ne mai kyau na farko, amma ko kusa bai isa ya dakatar da tarzomar da ta barke a kasar ba. Iyakar abin da zai yi, shine zai jinkirta abin ne kawai.”












