Daga Hassan Umar Gwammaja
Haɗakar jam’iyyar hammaya ta ADC a Najeriya ta tabbatar da naɗin Tsohon Shugaban Majalisar Dattawan Ƙasar, Sanata David Mark a matsayin sabon shugabanta na ƙasa.
Sanata David Mark, ya bayyana cewa ƙawancen ADC, haɗaka ce da ta shafe watanni ana tattaunawa domin samar da ita.
Ya ambato manyan matslolin tsaron da ke addabar jahohin Kaduna da Katsina da Zamfara da Sokoto da Borno da Yobe da sauran su, da cewa duk wani da ya damu da halin da ake ciki mai alaƙa da hakan, to ya amince da shiga wannan haɗaka ta su.
Ya ce duk waɗanda suka hallara a taron da zuciya ɗaya suka amince da dunƙulewar.
Wannan haɗaka dai an daɗe ana hanƙoron ganin an yi ta domin tunkarar jam’iyyar APC mai mulkin Najeriya, duba da cewar al’ummar Arewacin ƙasar sun gaji da irin salon mulkin gwamnatin shugaba Tinubu, wanda babu komai a cikinsa sai yunwa, fatara, talauci da kuma tsadar rayuwa, uwa uba ga rashin tsaro sai ɗaukar sabon salo yake yi Arewacin ƙasar.
Masu sharhi kan al’amuran siyasa dai na ganin cewar matuƙar al’ummar Arewa ba dunƙulewa suka yi ba a jam’iyya guda to zai yi wahala a iya kayar da gwamnatin mai ci.












