Ƙungiyar lauyoyin Najeriya ta buƙaci kotu da ta soke takardar shaidar NYSC da aka ba Hannatu Musawa da Kenny Ogungbe A ƙarar da ta shigar a kan ministar da Kenny,
NBA ta bayyana cewa hidimar ƙasar da Hannatu da Ogungbe suka yi bayan sun haura shekara 30 ta haramta
Don haka ƙungiyar ta buƙaci Shugaba Tinubu da ya kori ministar ta al’adu sannan kuma ta buƙaci kotun da ta kiyaye tanade-tanaden dokar NYSC
Sashen NBA kan buƙatun jama’a da dokar ci gaba ya kuma buƙaci kotun da ta tilasta wa hukumar NYSC ta soke takardar shaidar da aka ba Musawa da wani mai tallata waƙa, Kenny Ogungbe.
Kamar yadda shafin jaridar The Punch ya ruwaito, ƙungiyar ta yi zargin cewa bayar da takardar shaidar ya saɓa wa tanadin dokar NYSC ta Cap N84.LFN 2024.
Waɗanda suka shigar da ƙarar sun haɗa da shugaban NBA-SPIDEL, John Aikpokpo-Martins, da sakataren NBA-SPIDEL, Funmi Adeogun, rahoton New Telegraph ya tabbatar.
Musawa, Ogungbe, NYSC, da kuma gwamnatin tarayyar Najeriya sune wadanda ake tuhuma na farko zuwa na huɗu a cikin ƙarar.










