PYONGYANG – Kasar China ta sake jaddada cikakken goyon bayanta ga Koriya ta Arewa yayin wata babbar ziyara da shugaba Xi Jinpin ya kai Pyongyang, karo na farko cikin shekaru bakwai. Wannan na nuna muhimmancin dangantakar da ke tsakanin kasashen biyu a lokacin da ake fuskantar kalubalen siyasa da tsaro a duniya.
A yayin ganawar shugabannin Jinpin ya bayyana muhimmancin ci gaba da karfafa alakar kasashen biyu tare da fadada hadin gwiwa a fannoni daban-daban da suka shafi muradunsu na bai daya. Beijing ta bayyana dangantakar da Pyongyang a matsayin wacce ta dade tana da tushe mai karfi.
China ta kuma isar da sako mai karfi na goyon baya, inda ta ce ba za ta ja da baya ba wajen kare muradun da kasashen biyu ke da su tare. Wannan furuci na nuna aniyar Beijing na kara hada kai da Koriya ta Arewa a yayin da ake samun karin gasa tsakanin manyan kasashe na Duniya
Ana sa ran wannan ziyara za ta kara karfafa hulɗar diflomasiyya tsakanin kasashen biyu tare da bude kofar zurfafa hadin gwiwa a fannonin kasuwanci, tsaro da harkokin yankin. Masu nazari na kallon ziyarar a matsayin wata muhimmiyar alama ta ci gaba da goyon bayan da China ke bai wa Koriya ta Arewa duk da matsin lambar kasa da kasa da takunkuman da ake mata.












