Ministan Harkokin Cikin Gida na Pakistan, Mohsin Naqvi, wanda ke gudanar da ziyara a birnin Tehran na Iran, ya isar da wani sako ga gwamnatin Iran inda ya gargade ta kan kara tsananta rikici a hanyoyin jigilar kayayyaki ta ruwa. Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da ake fuskantar tashin hankali a yankin Gabas ta Tsakiya.
Rahotanni sun nuna cewa Naqvi ya bayyana damuwa kan yiwuwar rikicin ya shafi harkokin sufurin jiragen ruwa da kasuwancin kasa da kasa, yana mai jaddada muhimmancin kiyaye zaman lafiya da tsaro a hanyoyin ruwa na yankin.
Haka kuma, ministan ya bukaci Iran da ta bayyana matsayinta kan bukatun da Amurka ta gabatar mata cikin gaggawa, domin rage rashin tabbas da kuma samar da damar ci gaba da tattaunawar diflomasiyya tsakanin bangarorin biyu.
A wani sako da ya isar wa shugabannin Iran, Babban Hafsan Sojin Pakistan, Janar Asim Munir, ya bukaci Tehran da ta yi amfani da damar da ake da ita a yanzu wajen cimma yarjejeniya, yana mai cewa hakan zai iya taimakawa wajen tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin.











