Yayin da ƴan Najeriya ke fatan samun sauki, matatar man Ɗangote mai ƙarfin ta ce gangar ɗanyen mai 650,000 za ta fara sayar da man fetur
Mataimakin shugaban rukunin masana’antun Ɗangote, Devakumar Edwin ya ce man fetur zai shiga kasuwa a Yuli kamar yadda aka yi alƙawari
Edwin ya ce matatar Dangote za ta samar da isasshen man fetur, kalanzir, dizal da man jirgi a Najeriya har ma a a fitar da su zuwa ƙasashen waje
A cewarsa, hakan zai taimaka wajen kawo ƙarshen wahalhalun fetur a nahiyar Afirka da kuma tace ɗanyen man da ake haƙowa a cikin gida.
Mista Edwin ya ce kamfanin yana da burin samar da ingantaccen tsarin ci gaban masana’antu, samar da ayyukan yi da wadatar tattalin arziki.
Ya ce duk kayan da matatar take fitar wa suna da inganci kuma sun cika dukan sharuɗɗa da ƙa’idojin aiki na ƙasa da ƙasa, rahoton Leadership.











