DAGA HASSAN UMAR GWAMMAJA
An gudanar da taro ne a Babban Masallacin Juma’a Na Khalifa Sheikh Ishaq Rabiu dake Goron Dutse a birnin Kano.
Taron Khatamar Al’qur’anin mai tsarki wanda Khalifa Alhaji Nafi’u Ishaq Rabi’u ya shirya domin yiwa kasa da jihar Kano Addua’ar Samun zaman lafiya da karuwar arziki da samun rangwame a halin da al’ummar Najeriya suke ciki a yanzu na matsin tsanananin rayuwa.
Manyan Malamain Addinnin Musulunci da Shehunnai sun gabatar da addu’oi ta musamman a lokacin wannan taro na Khatamar karatun Al’qur’ani Mai Girma guda dubu uku (3,000)
Mai Martaba Sarkin Kanon Alhaji Aminu Ado Bayero ya samu rakiya dubun nan magoya baya da masoya zuwa wajan taron.












