By:Khadija Muhammad Maitaya
Date:August 11,2026
Kwamishinan Yada Labarai da Harkokin Cikin Gida na Jihar Kano, Kwamared Ibrahim Abdullahi Waiya, ya yi kira ga al’ummar jihar da su guji yada jita-jita da bayanan da ba su da tushe, musamman kan shirin Auren Gata da gwamnatin jihar ta gudanar.
Kwamishinan ya yi wannan kiran ne yayin wata ganawa da ƙungiyar matasan Limaman Masallatan Juma’a na Kano, inda ya jaddada muhimmiyar rawar da limamai ke takawa wajen wayar da kan jama’a da kuma tabbatar da zaman lafiya a jihar.
Waiya ya bayyana damuwarsa kan yadda wasu mutane ke yaɗa hotunan wasu dattawa a kafafen sada zumunta, tare da ikirarin cewa an ɗaura musu aure a ƙarƙashin shirin Auren Gata na gwamnatin jihar.
A cewarsa, bincike ya nuna cewa wasu daga cikin mutanen da ake yaɗa hotunansu tsofaffin jami’an Hisbah ne da suka yi ritaya daga aiki, ba sababbin Angwayen da aka ɗaura wa aure a ƙarƙashin shirin Auren Gata ba ne.
Ya ce yaɗa bayanai ba tare da tabbatar da sahihancinsu ba na iya haifar da ruɗani, rashin fahimta da kuma tayar da hankalin jama’a.
Kwamishinan ya buƙaci al’umma da su riƙa tantance sahihancin duk wani bayani kafin su yaɗa shi, tare da mayar da hankali wajen yaɗa saƙonnin da za su amfani al’umma.
Ya kuma jaddada cewa limaman Masallatan Juma’a suna da babbar rawar da za su taka wajen wayar da kan jama’a kan illolin jita-jita, da kuma ƙarfafa zaman lafiya, haɗin kai da fahimtar juna tsakanin al’ummar Kano.
Kwamared Waiya ya ce shirin Auren Gata yana da muhimmiyar manufa, wato tallafa wa waɗanda aka shirya wa auren tare da rage musu nauyin kuɗaɗen da ke tattare da gudanar da aure.
Ya ƙara da cewa ya kamata limamai da sauran masu ruwa da tsaki su ci gaba da wayar da kan jama’a kan manufar shirin, domin kauce wa yaɗa bayanan da ba su dace ba.
Kwamared Ibrahim Abdullahi Waiya ya yi kira ga al’ummar Kano da su haɗa kai da gwamnati wajen tabbatar da zaman lafiya da fahimtar juna, tare da tabbatar da cewa duk wani bayani da za a yaɗa sahihi ne kuma mai amfani ga al’umma.
A nasa jawabin shugaban Ƙungiyar Matasan Limamai Masu Son Ci gaban Jihar Kano ya jaddada goyon bayansu ga Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf, bisa yadda yake gudanar da ayyuka a jihar.
Ya ce sun kawo wannan ziyara ne domin ƙarfafa tafiyar mai girma Gwamna, bisa yadda ya gudanar da shirin Auren Gata a jihar, da kuma ayyukan raya ƙasa da yake aiwatarwa a faɗin jihar Kano.
Haka zalika, ya ƙara da cewa sun kawo ziyarar ne ƙarƙashin jagorancin Kwamishinan Yaɗa Labarai da Harkokin Cikin Gida, Kwamared Abdullahi Waiya, bisa yadda yake shiga cikin al’amuran malamai a jihar. Ya ce a shirye suke su ci gaba da yi wa gwamnatin addu’a domin ci gaban Jihar Kano.









