DAGA HASSAN UMAR GWAMMAJA
Koken nasu ya samo asali ne daga rashin aiwatar da yarjejeniya 16 da aka kulla tsakanin kungiyoyin kwadago (NLC da TUC) da gwamnatin tarayya a ranar 2 ga Oktoba, 2023.
Shugabannin kungiyoyin NLC da TUC sun bayyana damuwarsu da cewa, duk da kokarin da kungiyoyin kwadago ke yi na inganta zaman lafiya a ma’aikatu, ga dukkan alamu gwamnati ba ta damu da wahalhalun da al’umma suke ciki ba .
NLC da TUC, a cikin wata sanarwa da suka fitar, sun koka da cewa “abin takaici ne yadda aka tilasta mana daukar irin wadancan matakan, amma rashin kula da walwalar ‘yan kasa da ma’aikatan Najeriya da kuma tsananin wahala ya sa ba mu da zabi sai mun yi haka.”
“Sakamakon wannan ci gaba tare da sanin muhimmancin tabbatar da tsaro da kare hakki da mutuncin ma’aikatan Najeriya da ‘yan kasa, kungiyar NLC da TUC sun ba da wa’adi ga gwamnatin tarayya da ta mutunta yarjejeniya cikin kwanaki 14 daga gobe, ranar 9 ga Fabrairu 2024.”











