Kungiyar yantebura dake IBB jikin masallacin Idi na birnin Kano ta bayyana cewa ba dagayya gwamnatin jihar ta rushe rumfunan mambobinta ba
Bayanin hakan na dauke ne a wani jawabi da shugabannin kungiyar suka fitar a wani taron manema labarai da suka gudanar.
Shugaban kungiyar kwamared Zayyanu Murtala a jawabinsa ya godewa gwamnan jihar kano Abba Kabir Yusuf da ya basu dama suka ga a da shi Dan jin koken su ta hanyar S A 1 da S A 2.
Kazalika shima jagoran iyayen kungiyar, Yakubu Tijjani Muhammad kantudun Madabo, ya bayyana irin Farin cikin da suka sami Kansu bayan da gwamna Abba Kabir ya basu tabbacin gyara musu teburan da aka rushe musu cikin kuskure.
A nasa jawabin mataimakin shugaban kungiyar, Saminu Ibrahim ya karyata masu cewa gwamnatin kano ta rushe gurin nasu ne domin ta tashe su inda yace da haka ne sai dare ya yi za ta zo ta rushe kamar yadda ya gudana a gwamnatin Ganduje
Shima sakataren kudi na kungiyar Muhammad a jawabin sa ya jaddada cewa zasu bi umarnin da gwamna Abba Kabir ya basu na tsaftace gurin tare da kaucewa kasa kaya akan titi
Daga karshe Shugabannin sun godewa gwamna Abba Kabir da S A 1 da S A 2 da shugaban KNUPDA da shugaban ma’aikatan fadar gwamnatin kano da duk wadanda suka yi gwauro da Mari wajan shigar da koken su ga mai girma gwamna.











