Sojojin Najeriya sun ce sun kashe ‘ƴan ta’adda 254 tare da kama guda 264 a ayyukan da ta gudanar cikin mako ɗaya a faɗin ƙasar.
Daraktan yaɗa labaru cibiyar tsaro ta Najeriya, Mano Janar Edward Buba ne ya bayyana haka a wata ganawa da manema labaru a yau Juma’a.
Ya ce “shirye-shiryen da muke aiwatarwa na yaƙi da ƴan ta’adda da masu tayar da ƙayar baya ya hana masu aikata miyagun laifuka cimma manufofinsu.”
Najeriya dai na fama da matsalolin tsaro a kowane ɓangare na ƙasar.












