Shugaban kasar Amurka, Joe Biden, ya bayyana haƙura da takararta ta shugabancin Amurka a wa’adin mulki karo na biyu.
Shugaban ya bayyana hakan ne cikin jawabin da ya yi a wani taron manema labarai, shugaban ya ce ya yi hakan ne domin ”masalahar jam’iyyarsa da kuma ƙasarsa”.
Ya ce cikin shekara uku da rabi da ya yi yana jagorantar Amurka, ƙasar ta samu gagarumin ci-gaba.
”A yau Amurka na da ƙarfin tattalin arziki a duniya, mun kafa tarihi a fannin zuba jari domin sake gina ƙasarmu”.
A baya-bayan nan dai shugaban ya fuskanci matsin lamba daga manyan ‘yan jam’iyyarsa da ke kiraye-kirayen ya haƙura da takara, tun bayan rashin kataɓus a muhawarsa da Donald Trump.












