Daga Hassan Umar Gwammaja
Yanzu haka dai ta leko ta koma ga jam’iyyar Labour a jihar Bauchi wanda ta samu kuri’u mafi yawa a zaben kansilan Bogoro da aka gudanar a mazabar Lusa B da ke karamar hukumar Bogoro, duk da cewa ba ta fitar da dan takara ba a ya yin zaben.
Bisa hakan, hukumar zabe mai zaman kanta ta jihar Bauchi, BSIEC, ta ayyana ‘yar takarar jam’iyyar PDP mai mulki, Lucy Ahmadu Yusuf, wadda ta zo a matsayi na biyu, a matsayin wanda ta lashe zaben kuma zababbiyar kansila mai wakiltar mazabar Lusa B.
Da yake sanar da sakamakon zaben a cibiyar tattara sakamakon zaben da ke Bogoro, jami’in zabe, Daniel Gambo, ya bayyana cewa jam’iyyar Labour, ba tare da dan takara ba, ta samu kuri’u 2,200 ya yin da ‘yar takarar Jam’iyyar PDP Lucy Ahmadu Yusuf ta samu kuri’u 2,168.
Dan takarar jam’iyyar APC, Mbam Masoyi, ya zo na uku a zaben da kuri’u 275.











