Gwamnatin jihar Legas ta ce ta kwace Baburan Okada 668 a cikin sati guda saboda karya dokar hana zirga-zirgarsu a manyan hanyoyi, tare da kama mutum bakwai da ake zargi da yunkurin hana jami’ai gudanar da aikinsu.
Hukumar Lura da Muhalli da Laifuffuka ta jihar (Task Force) ce ta jagoranci wannan aikin, inda ta kai samame a wurare daban-daban da ake zargin masu Baburan Okada na haddasa matsalolin tsaro da hatsari ga jama’a.
Shugaban hukumar, CSP Adetayo Akerele, ya bayyana haka a cikin wata sanarwa da aka fitar ranar Lahadi ta bakin mai magana da yawun hukumar, Abdulraheem Gbadeyan.
Ya ce wannan mataki wani ɓangare ne na ci gaba da ƙoƙarin tabbatar da doka kan haramcin zirga-zirgar babura a manyan hanyoyin da gwamnati ta ware
A cewar sa, duk da gargadi sau da dama, masu babura na ci gaba da karya doka, abin da ya ce na jefa rayuka da dukiyar jama’a cikin barazana.
Shugaban hukumar ya jaddada cewa dukkan baburan da aka kwace za a gurfanar da su a kotu, sannan daga bisani a murƙushe su, bisa ga dokokin jihar.












