• About
  • Advertise
  • Privacy & Policy
  • Contact
AKSAM
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO
No Result
View All Result
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO
No Result
View All Result
AKSAM
No Result
View All Result

Gwamnan kano ya sake tauna Aya ga masu niyar kawo tashin-tashina a jihar

aksam by aksam
May 29, 2024
Reading Time: 1 min read
0
Home LABARAI
ADVERTISEMENT
467
SHARES
1.5k
VIEWS
Share on FacebookShare on Twitter

Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf ya haramta gudanar “duk wani nau’in taro da zimmar zanga-zanga” a faɗin jihar yayin da ake ci gaba da tirka-tirka tsakanin sarakunan Kano biyu.

Gwamnan ya yi iƙirarin cewa ‘yan jam’iyyar adawa na yunƙurin ɗaukar nauyin wasu ɗalibai daga wasu jihohi don tayar da hankali a jihar, kamar yadda mai magana da yawunsa Sanusi Bature ya bayyana cikin wata sanarwa a yau Laraba.

RelatedPosts

Gwamnan Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf Ya Sanya Ranar Talata 05 GA watan Mayu 2026, A Matsayin Ranar Da Zai Jagoranci Rantsar Da Murtala Sule Garo A Matsayin Mataimakin Gwamnan

Shekara Kwana: Shekaru 24 Kenan Da Hatsarin Jirgin Sama A Unguwar Gwammaja Dake Jihar Kano

NDLEA Ta Kama Mutane 6, Ta Rushe Maboyar Miyagun Kwayoyi a BUK Old Site Kano

“Gwamnan ya bai wa ‘yansanda, da ‘yansandan farin kaya, da jami’an tsaron Civil Defence umarnin kamawa da tsarewa da tuhumar duk wani mutum ko ƙungiya da suka shiga zanga-zanga a kan titunn Kano,” in ji sanarwar.

Duk da cewa ana ci gaba da zama lafiya da kuma harkoki kamar yadda aka saba a birnin, kawunan Kanawan sun rarrabu game da sarkin da ke mulkin masarautar jihar tsakanin Muhammadu Sanusi II da kuma Aminu Ado Bayero.

Yanzu haka kowannensu na da umarnin kotu biyu-biyu da ke hana jami’an tsaro fitar da shi daga fada ko kuma sauke shi a matsayin sarkin Kano. Sanusi na zaman fada a fadar Gidan Dabo, yayin da Aminu ke nasa zaman a gidan sarki na Nassarawa.

A cewar Sanusi Bature, Gwamna Abba Kabir ya ce: “Mun samu bayanan sirri cewa wasu manyan ‘yan jam’iyyar adawa na shirin ɗaukar nauyin ɗalibai da ‘yansiyasa daga wasu jihohin arewa maso yamma don haddasa fitina ta hanyar fakewa da zanga-zangar goyon bayan Sarki Aminu Ado Bayero.

“Gwamnatin jiha ta haramta zanga-zanga, da kowane irin maci, sannan duk mutumin da aka gani yana aikata hakan za a kama shi nan take.”

Share187Tweet117SendShare
ADVERTISEMENT
Previous Post

Majalisar Dokoki ta nemi sanata Abdul Ningi ya dawo bakin aiki

Next Post

Zargin neman aikata badala da matar Aure wani magidanci ya tsinci talatarsa a laraba

aksam

aksam

RelatedPosts

Gwamnan Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf Ya Sanya Ranar Talata 05 GA watan Mayu 2026, A Matsayin Ranar Da Zai Jagoranci Rantsar Da Murtala Sule Garo A Matsayin Mataimakin Gwamnan
LABARAI

Gwamnan Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf Ya Sanya Ranar Talata 05 GA watan Mayu 2026, A Matsayin Ranar Da Zai Jagoranci Rantsar Da Murtala Sule Garo A Matsayin Mataimakin Gwamnan

by aksam
May 4, 2026
Shekara Kwana: Shekaru 24 Kenan Da Hatsarin Jirgin Sama A Unguwar Gwammaja Dake Jihar Kano
LABARAI

Shekara Kwana: Shekaru 24 Kenan Da Hatsarin Jirgin Sama A Unguwar Gwammaja Dake Jihar Kano

by aksam
May 4, 2026
NDLEA Ta Kama Mutane 6, Ta Rushe Maboyar Miyagun Kwayoyi a BUK Old Site Kano
LABARAI

NDLEA Ta Kama Mutane 6, Ta Rushe Maboyar Miyagun Kwayoyi a BUK Old Site Kano

by Khadija Maitaya
May 4, 2026
Tsohon Dan Takarar Shugaban Kasa A  Jam’iyyar Labour Party, Peter Obi, Ya Sanar Da Ficewarsa Daga  Jam’iyyar Haɗaka Ya ADC
LABARAI

Tsohon Dan Takarar Shugaban Kasa A Jam’iyyar Labour Party, Peter Obi, Ya Sanar Da Ficewarsa Daga Jam’iyyar Haɗaka Ya ADC

by aksam
May 3, 2026

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Recommended.

An hana ganduje shiga wurin manyan baƙi, Aranar rantsuwa

An hana ganduje shiga wurin manyan baƙi, Aranar rantsuwa

May 29, 2023
Zargin samadafadi na 10bn, EFCC zata gurfanar da wani tsohon gwamna a gaban kotu

Zargin samadafadi na 10bn, EFCC zata gurfanar da wani tsohon gwamna a gaban kotu

February 22, 2024
ADVERTISEMENT

Trending.

Mu Na Gayyatar  ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Gurin Daurin Auren:- Comr.  Usaini Sani Adamu !!!

Mu Na Gayyatar ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Gurin Daurin Auren:- Comr. Usaini Sani Adamu !!!

April 24, 2026
Ga Sakon Bangajiya Daga: Angon Umar SA’ID

Ga Sakon Bangajiya Daga: Angon Umar SA’ID

April 20, 2026
Shekara Kwana: Shekaru 24 Kenan Da Hatsarin Jirgin Sama A Unguwar Gwammaja Dake Jihar Kano

Shekara Kwana: Shekaru 24 Kenan Da Hatsarin Jirgin Sama A Unguwar Gwammaja Dake Jihar Kano

May 4, 2026
Muna Gayyatar ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Daurin Auren;- UMAR SA’ID

Muna Gayyatar ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Daurin Auren;- UMAR SA’ID

April 17, 2026
Atiku, Kwankwaso , Obi Sun Jagoranci Zanga-Zanga A Babban Birnin Tarayya Abuja

Atiku, Kwankwaso , Obi Sun Jagoranci Zanga-Zanga A Babban Birnin Tarayya Abuja

April 8, 2026

Aksam Hausa

AKSAM MEDIA is a company which designed as online News Platform and other activities related to develop society.

The AKSAM MEDIA created since November 2019 and it does many activities as News publishes it publishes a Hausa News And English News.

No Result
View All Result
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO

© 2023 Aksam media