Daga Hassan Umar Gwammaja
Gwamnan ya bayyana haka ne yayin da yake bude cibiyar koyon dinki dake karamar hukumar Kura.
Gwamna Abba Kabir Yusuf wanda ya ce matasa 240 ne zasu amfana da shirin a Karon farko yace gwamnatinsa zata samar da kyakkyawan yanayin da zai bawa matasan da aka koyar damar cigaba da dinki a matsayin sana’ar dogaro da kawunansu.
Ya nuna rashin jin dadinsa bisa yadda gwamnatin data gabata ta yi watsi da irin wannan cibiyoyin koyar da matasa tare da kwashe kayan da aka zuba musu, inda ya jaddada cewa gwamnatinsa zata kwato dukkanin kayan da aka kwashe.
A jawabinsa, kwamishinan Kasuwanci Da Masana’antu Alhaji Shehu Wada Sagagi yace gwamnatin jiha zata farfado da masana’antun jihar kano ta Yadda jihar zata dinga fitar Kaya zuwa kasashen duniya.










