Daga; Hassan Umar Gwammaja
Rahotanni daga majiyoyi masu tushe sun nuna cewa Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, na ci gaba da tattara bayanai da shawarwari domin tabbatar da yiwuwar naɗa Murtala Sule Garo a matsayin sabon mataimakinsa.
Majiyoyin sun ce gwamnan na gab da kammala tattaunawa da muhimman masu ruwa da tsaki, musamman daga jam’iyyar All Progressives Congress (APC), domin cimma matsaya kan wannan mataki.
A baya-bayan nan dai an samu ɗan tangarda tsakanin wasu ƙusoshin siyasa da gwamnan ya tarar, lamarin da ya haifar da saɓani kan batun wanda zai maye gurbin mataimakin gwamna. Sai dai rahotanni sun nuna cewa, bayan jerin ganawa a ɓoye da aka gudanar a lokuta daban-daban, an samu daidaito tare da rage duk wata barazana ta rikici.
Wata majiya mai kusanci da gidan gwamnati, wadda ta nemi a sakaya sunanta, ta shaida cewa gwamnan ya gudanar da muhimman ganawa da jagororin siyasar Kano ta Kudu, inda ya samu goyon bayansu kan zaɓin Garo domin riƙe mukamin mataimakin gwamna.
Hakazalika, an rawaito cewa wasu daga cikin jiga-jigan siyasa da ke ƙarƙashin tsohon gwamnan Kano kuma tsohon shugaban APC na ƙasa, Abdullahi Umar Ganduje, sun nuna amincewa da wannan zaɓi, duk da cewa akwai wasu ‘yan tsiraru da ke nuna adawa bisa dalilai na siyasa.
Murtala Sule Garo, wanda ya taɓa zama kwamishinan ƙananan hukumomi a jihar, shi ne kuma tsohon ɗan takarar mataimakin gwamna na APC a zaɓen 2023. Yanzu haka ana ganin yana da ƙarfi wajen karɓar wannan muƙami, bayan murabus ɗin da tsohon mataimakin gwamnan, Aminu Abdussalam Gwarzo, ya yi a ƙarshen makon da ya gabata.
Har zuwa lokacin haɗa wannan rahoto, gwamnatin jihar ba ta fitar da wata sanarwa a hukumance ba dangane da wannan batu.












