• About
  • Advertise
  • Privacy & Policy
  • Contact
AKSAM
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO
No Result
View All Result
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO
No Result
View All Result
AKSAM
No Result
View All Result

Gwamna Abba Na Shirin Naɗa Murtala Garo A Matsayin Mataimaki:— Rahotanni

aksam by aksam
April 1, 2026
Reading Time: 2 mins read
0
Home SIYASA
ADVERTISEMENT
466
SHARES
1.5k
VIEWS
Share on FacebookShare on Twitter

 

Daga; Hassan Umar Gwammaja

RelatedPosts

Tsohon Gwamnan Jihar Kano, Rabiu Musa Kwankwaso, Ya Koma Jam’iyyar National Democratic Congress (NDC) A Hukumance; Inda Ya Karɓi Katin Zama Mamba Na Jam’iyyar

Gwamnan Jihar Bauchi, Sanata Bala Mohammed Ya Fice Daga Jam’iyar PDP

Wasu Dalilin Da Suka Sa Kwankwaso Ke Shirin Ficewa Daga Jam’iyyar ADC

Rahotanni daga majiyoyi masu tushe sun nuna cewa Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, na ci gaba da tattara bayanai da shawarwari domin tabbatar da yiwuwar naɗa Murtala Sule Garo a matsayin sabon mataimakinsa.

 

Majiyoyin sun ce gwamnan na gab da kammala tattaunawa da muhimman masu ruwa da tsaki, musamman daga jam’iyyar All Progressives Congress (APC), domin cimma matsaya kan wannan mataki.

A baya-bayan nan dai an samu ɗan tangarda tsakanin wasu ƙusoshin siyasa da gwamnan ya tarar, lamarin da ya haifar da saɓani kan batun wanda zai maye gurbin mataimakin gwamna. Sai dai rahotanni sun nuna cewa, bayan jerin ganawa a ɓoye da aka gudanar a lokuta daban-daban, an samu daidaito tare da rage duk wata barazana ta rikici.

 

Wata majiya mai kusanci da gidan gwamnati, wadda ta nemi a sakaya sunanta, ta shaida cewa gwamnan ya gudanar da muhimman ganawa da jagororin siyasar Kano ta Kudu, inda ya samu goyon bayansu kan zaɓin Garo domin riƙe mukamin mataimakin gwamna.

 

Hakazalika, an rawaito cewa wasu daga cikin jiga-jigan siyasa da ke ƙarƙashin tsohon gwamnan Kano kuma tsohon shugaban APC na ƙasa, Abdullahi Umar Ganduje, sun nuna amincewa da wannan zaɓi, duk da cewa akwai wasu ‘yan tsiraru da ke nuna adawa bisa dalilai na siyasa.

 

Murtala Sule Garo, wanda ya taɓa zama kwamishinan ƙananan hukumomi a jihar, shi ne kuma tsohon ɗan takarar mataimakin gwamna na APC a zaɓen 2023. Yanzu haka ana ganin yana da ƙarfi wajen karɓar wannan muƙami, bayan murabus ɗin da tsohon mataimakin gwamnan, Aminu Abdussalam Gwarzo, ya yi a ƙarshen makon da ya gabata.

 

Har zuwa lokacin haɗa wannan rahoto, gwamnatin jihar ba ta fitar da wata sanarwa a hukumance ba dangane da wannan batu.

Share186Tweet117SendShare
ADVERTISEMENT
Previous Post

HAJJIN 2026: Irin Halin Da Sama Da Maniyyata 1,000 Suke Ciki A Jihar Kaduna

Next Post

Donal Trump Ya Sanya Wa’adi Dakatar Da Yaki Da Iran Ko Da Babu Yarjejeniya

aksam

aksam

RelatedPosts

Tsohon Gwamnan Jihar Kano, Rabiu Musa Kwankwaso, Ya Koma  Jam’iyyar National Democratic Congress (NDC)  A Hukumance; Inda Ya Karɓi Katin Zama Mamba Na Jam’iyyar
SIYASA

Tsohon Gwamnan Jihar Kano, Rabiu Musa Kwankwaso, Ya Koma Jam’iyyar National Democratic Congress (NDC) A Hukumance; Inda Ya Karɓi Katin Zama Mamba Na Jam’iyyar

by aksam
May 3, 2026
Gwamnatin Jihar Bauchi Ta Umarci  Duk Masu Riƙe Da Mukaman Siyasa Dake Da Niyyar Tsayawa Takara Dasu Yi Murabus Kafin Ranar Juma’a 24 ga Watan Afrilu 2026
SIYASA

Gwamnan Jihar Bauchi, Sanata Bala Mohammed Ya Fice Daga Jam’iyar PDP

by aksam
May 2, 2026
Ba Za Mu Bawa Kwankwaso Tikitin Takarar Shugabancin Kasa A Jam’iyyarmu— NNPP
SIYASA

Wasu Dalilin Da Suka Sa Kwankwaso Ke Shirin Ficewa Daga Jam’iyyar ADC

by aksam
May 2, 2026
Masu Ruwa Da Tsaki A  APCn Kano Sun Amince Da Takarar Abba da Tinubu Karo Na Biyu A Zaɓen 2027
SIYASA

Masu Ruwa Da Tsaki A APCn Kano Sun Amince Da Takarar Abba da Tinubu Karo Na Biyu A Zaɓen 2027

by aksam
May 1, 2026

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Recommended.

Faransa ta janye dukkan ajiyar zinariyarta daga bankin Federal Reserve Bank of New York.

Faransa ta janye dukkan ajiyar zinariyarta daga bankin Federal Reserve Bank of New York.

April 7, 2026
Kwamishinan Jinkai Da Walwallar Jama’a Comred Markus Yunana Barda Ya Aika Da Sakon Barka Da Sallah Ga Gwamna Uba Sani, Mai Martaba Sarkin Jama’a Da Kuma Sauran Al’umma Musulmi

Kwamishinan Jinkai Da Walwallar Jama’a Comred Markus Yunana Barda Ya Aika Da Sakon Barka Da Sallah Ga Gwamna Uba Sani, Mai Martaba Sarkin Jama’a Da Kuma Sauran Al’umma Musulmi

June 10, 2025
ADVERTISEMENT

Trending.

Mu Na Gayyatar  ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Gurin Daurin Auren:- Comr.  Usaini Sani Adamu !!!

Mu Na Gayyatar ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Gurin Daurin Auren:- Comr. Usaini Sani Adamu !!!

April 24, 2026
Ga Sakon Bangajiya Daga: Angon Umar SA’ID

Ga Sakon Bangajiya Daga: Angon Umar SA’ID

April 20, 2026
Shekara Kwana: Shekaru 24 Kenan Da Hatsarin Jirgin Sama A Unguwar Gwammaja Dake Jihar Kano

Shekara Kwana: Shekaru 24 Kenan Da Hatsarin Jirgin Sama A Unguwar Gwammaja Dake Jihar Kano

May 4, 2026
Muna Gayyatar ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Daurin Auren;- UMAR SA’ID

Muna Gayyatar ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Daurin Auren;- UMAR SA’ID

April 17, 2026
Atiku, Kwankwaso , Obi Sun Jagoranci Zanga-Zanga A Babban Birnin Tarayya Abuja

Atiku, Kwankwaso , Obi Sun Jagoranci Zanga-Zanga A Babban Birnin Tarayya Abuja

April 8, 2026

Aksam Hausa

AKSAM MEDIA is a company which designed as online News Platform and other activities related to develop society.

The AKSAM MEDIA created since November 2019 and it does many activities as News publishes it publishes a Hausa News And English News.

No Result
View All Result
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO

© 2023 Aksam media