Masana sun bayyana cewa ya kamata gwamnatin Ghana ta yi la’akari da bayar da lasisi ga masu ƙera bindigogi na gargajiya domin gano da kuma bibiyar yaduwarsu ta haramtacciyar hanya. Wannan mataki, in ji su, zai taimaka wajen rage safarar makamai a cikin ƙasar.
A watan Yuli, masanin tsaro Adam Bonaa ya yi kira da a sabunta dokokin makamai na Ghana da suka wuce shekaru 50 da kafuwa. Kiran nasa ya biyo bayan mutuwar dalibi a wani makarantar sakandare da ke yankin Arewa, bayan harbin wuce gona da iri daga wani biki a unguwa.
Bonaa ya ce dokokin da ake amfani da su yanzu sun yi ƙasa wajen kare rayukan jama’a, tare da bai wa masu safarar makamai damar ci gaba da aikata laifuka ba tare da tsoro ba.
A nasa bangaren, Mataimakin Ministan Cikin Gida, Ebenezer Okletey Terlabi, ya bayyana cewa akwai buƙatar takaita gibin tsaro ta hanyar inganta tsare-tsaren dokokin makamai a fadin ƙasar.
Terlabi ya jaddada cewa gwamnati za ta ci gaba da ƙoƙarin ganin Ghana ta zama ƙasa mai aminci, ba tare da tashin hankali na bindigogi ba, yayin taron duba Dokar Makamai ta ƙasa da aka gudanar a watan Yuli.











