Kungiyar rukunin masu masana,antu a jihar Kano, sun bukaci Gwamnatoci na matakai daban daban da su tallafa musu domin habaka harkokin masana,antu a fadin jihar.
Ibrahim bashir na sambo ,ya bayyana cewa, masu kananan masana,antu a jahar Kano, suna fuskantar kalubale da dama da suka hada da rashin ciniki da matsalar hasken wutal lantarki da kuma,tashin farashin Dala sakamakon kayayyakin aiyukansu da suka hadar da Injina, suna siyo sune daga kasashen ketare
Sakataran kongiyar ya bukaci gwamantoci a matakai daban daban dasu shiga domin farfado da kananan masana,antu duba da yadda masana ,antun suke Ragewa Gwamnati Nauye nauye ta fannin daukar matasa Ayyukan yi.
Haka zalika , Na sambo ya shawarci yankungiyar da su ci gaba da baiwa gwamnati da kungiyoyi cikakken hadin kan da suka kamata domin bunkasa kananan masana,antu a jahar kano ,da makasa baki daya.
Daga karshe yayi kira da gwamnati data saukakamusu wajan biyan kudin haraji .











