Ministan yada labarai da wayar da kan jama’a na Najeriya, Alhaji Mohammed Idris Malagi ya ce, da gwamnati ba ta cire tallafin mai ba da wahalar da ake ciki a ƙasar ta fi haka a yanzu.
Ministan ya bayyana hakan ne yayin da yake kare matakin gwamnatin ƙasar na cire tallafin mai a yayin wata hira da tashar talabijin ta Channels.
Tun a jawabinsa na farko bayan rantsar da shi, a watan Mayun 2023, Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya bayyana cewa babu sauran tallafin mai.
Tun daga lokacin da shugaban ya sanar da janye tallafin man kayayyakin masarufi da sauran harkokin rayuwa a Najeriya suke ta tashin gwauron zabi, rayuwa take ta kara tsada ga jama’a.












