Wani dan sanda ya gamu da ajalinsa a ranar Alhamis a jihar Ebonyi lokacin da wasu ‘yan bindiga suka bude wuta kan tawagar ‘yan sanda da ke sintiri.
Lamarin ya faru ne a yankin Ngbo-Effium, wa da ya dade yana fama da hare-hare a karamar hukumar Ohaukwu.
Kakakin rundunar ‘yan sanda, Joshua Ukandu ya tabbatar da hakan a wata sanarwa da ya fitar ranar Juma’a a Abakaliki, babban birnin jihar, The Nation ta ruwaito.
A cewarsa: “Wasu ‘yan bindiga sun kai wa jami’an rundunar ‘yan sanda da ke sintiri a kan titin Ngbo-Effium hari ta hanyar amfani da wata mota kirar Toyota
Sienna” Ya ce jami’an ‘yan sandan sun yi artabu da ‘yan ta’addan kuma a fafatawar da suka yi ne daya daga cikin ‘yan sandan ya gamu da ajalinsa.
Ukandu ya kara da cewa wani kuma dan sanda ya samu rauni kuma yanzu haka yana samun kulawa a asibiti.
“Kwamishanan ‘yan sanda na jihar Ebonyi, CP Augustina Ogbodo ya aike da tawagar ‘yan sanda zuwa wurin da abin ya faru.
“Tawagar ta na kan bin diddigin ‘yan bindigar yayin da kuma aka dawo da zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin”, in ji shi.”











