Attajirin da ya fi kowa arziki a Afirka, Aliko Dangote, ya bayyana shirin zuba jarin kusan dala biliyan 2 a ƙasar Gambia domin bunƙasa bangaren makamashi. Wannan mataki na daga cikin ƙoƙarinsa na faɗaɗa manyan ayyukan samar da ababen more rayuwa a ƙasashen Afirka bayan Najeriya.
An sanar da wannan shiri ne bayan ganawar da Dangote ya yi da Shugaban ƙasar Gambia, Adama Barrow, a birnin Banjul yayin taron African Caucus 2026 da aka gudanar ranar Talata. Sanarwar Fadar Shugaban Ƙasar ta bayyana cewa shirin zai taimaka wajen ƙarfafa samar da wutar lantarki da inganta ajiyar man fetur a ƙasar.
Daga cikin manyan ayyukan da aka tsara akwai gina tashar samar da wutar lantarki ta hasken rana mai ƙarfin megawatt 250, tare da gina katafariyar cibiyar ajiyar man fetur ta zamani. Ana sa ran waɗannan ayyuka za su inganta tsaron makamashi da samar da isasshen wutar lantarki ga al’ummar Gambia.
Dangote ya je ganawar tare da Babban Daraktan First Bank Group, Olusegun Alebiosu, lamarin da ke nuna cewa ana ci gaba da tattaunawa kan hanyoyin samar da kuɗaɗen aiwatar da wannan babban shirin zuba jari.










