DAGA HASSAN UMAR GWAMMAJA
Hukumar ta bayyana cewa tun ranar Alhamis ta saki Murja bisa umarnin kotu.
Tun a daren jiya dai ake ta rade-radin an nemi Jarumar TikTok din Murja Kunya a gidan gyaran hali an rasa ta, wanda hakan tasa Ake zantuka da korafe-korafe akai musamman a dandalin sada zumunta.
Kakakin gidan gyaran hali na jihar Kano AC Misbahu Kofar Nassarawa ya shaidawa Daily Nigerian hakan a yau lahadi.
“Sananniyar ‘yar Tiktok Murja Ibrahim Kunya ba guduwa ta yi daga gidan yari ba mu ne muka sake ta bisa Umarnin kotu” inji Musbahu Kofar Nasarawa
A cewar sa, tun ranar Alhamis takarda ta zo daga kotu don neman a sake ta, kuma gidan yarin ya sake ta tun a ranar.
Ya ƙara da cewa kotu ce ta kawo ta ajiya a wajensu, kuma kotu ce ta ce su sake ta.












