Da aka shirya zaben ‘yan majalisa a kasar Fakistan, Hafiz Naeem Ur Rehman yana cikin wadanda aka sanar da nasararsu
‘Dan takaran ya fito yana shaidawa duniya cewa ba zai karbi kujerar siyasa ba, dalilinsa kuwa shi ne an shirya magudin zabe Saboda a ba shi nasara a zaben da aka yi,
Hafiz Naeem Ur Rehman ya ce an murde dubban kuri’un da aka ba abokin adawarsa












