DAGA HASSAN UMAR GWAMMAJA
Mahaifiyar yaron mai suna Hamida Sani Abdulrazaq, ta shaida wa BBC cewa ‘ba za ta iya bayyana irin kaɗuwar da take ciki ba, bayan tsinto gawar ɗan nata cikin mummunan yanayi’.
“Yarona ya bata ne da yammacin ranar Laraba muka yi ta cigiya bamu same shi ba; ana cikin haka ne kuma aka ce an ga gawarsa a karkashin Gada dake Zariya, bakinsa duk wani irin abu idonsa kuma duk Jini, “in ji ta”.
Ta ci gaba da cewa dan nata mai suna Ibrahim, yana da lalaurar kwakwalwa ya fita ne waje daga bisani kuma ba’a ganshi ba, sai dai ta ce bata da masaniyar an kwakule masa idanu kamar yadda wasu ke yadawa cewar an kwakule masa idanun, inda ta ce kawo yanzu ba’a samu nasarar kama wadanda suka kashe shi ba.
“Mu mun dauki kaddara daman kwananshi ne ya kare kawai dai wadanda suka kashe shi sune suka yi silar rasuwarsa; tuni aka yi jana’izarsa, “A cewar Hamida”.
To dai kakakin rundunar ‘yan sanda jihar Kaduna ASP Mansir Hassan ya tabbar da faruwar lamarin in da yace, sunanan suna bicike akan lamarin.










