Kungiyar Middle-Belt Forum ta ce ‘yan ta’adda sun rubuto wasika cewa za su kuma kai wani hari a jihar Filato
Mista Stanley Kavwam ya shaidawa duniya wannan da aka yi hira da shi a matsayinsa na shugaba a MBF
Ana zargin jami’an tsaron Najeriya da cafke marasa laifi, yayin da mutane su ke cigaba rayuwa cikin barazana
‘Yan ta’addar sun aikowa mutanen Pushit a karamar hukumar Mangu wasika cewa za su sake kawo hari bayan kashe mutane 195.
A yau Juma’a, 29 ga watan Disamba 2023 ne aka yi alkawarin kawo wani harin na dabam.
Jaridar Punch ta fitar da cewa Mataimakin shugaban kungiyar MBF na kasa, Stanley Kavwam, ya tabbatar da haka da aka yi wata hira da shi a gidan talabijin na Arise a jiya.
Kavwam ya ce wasu mutane da ba a san su ba sun jefo wasiku a garin Pushit, suna barazanar kawo wani mummunan harin a yau.
“A yayin da na ke tuki daga Jos zuwa nan, an kira ni cewa an aiko takarda zuwa kauyenmu ‘yan ta’adda za su kawo hari a ranar 29 ga Disamba












