Duka alkalai uka da suka saurari karar sun amince da hukuncin kotun farko wacce ta kori, karar sai da ta ce inda kotun baya ta ce za a iya cewa zaben bai kammalu ba kuskure ne.
Alkalan sun hakan bai taso ba kwatakwata domin tun farko jam’iyyar PDP da dan takaranta Isah Ashiru sun taf ka kuskure.
Kuskuren kuwa kamar yadda alkalan suka fadi shine akwai wani fom da ake cikawa kafin wani lokaci na a lokacin da ake shigar da kara wanda PDP da dan takaranta ba su shigar da shi ba da wuri har kwanakin mika fom din ya cika.
Bisa wannan dalilai kuwa ya sa ita kanta shari’ar bata da mazauni ballantana har a saurareta bisa dokar zabe da na kasa.
A dalilin haka ya sa kotu ta yi watsi da karar ta ce uba Sani ne gwamnan Kaduna wanda mutanen Kaduna suka zaba.
Cikin farin ciki, gwamna Uba ya jinjina wa Kotun sannan ya yaba wa alkalan kan wanna hukunci da suka yanke yana mai cewa kotu ta tabbatar wa mutanen Kaduna abinda suka zaba ne.
A karshe ya yi kira ga yan jam’iyyar adawa su zo a hada hannu domin ci gaban jihar Kaduna.












