Daga Khadija Muhammad Maitaya
Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya karɓi lambobin yabo da karramawa daga ƙungiyoyi da cibiyoyi daban-daban a yayin taron Majalisar Zartarwa ta Jihar Kano karo na 40 da aka gudanar a Fadar Gwamnatin Kano.
An karrama Gwamnan ne bisa jagoranci nagari da kuma irin nasarorin da gwamnatinsa ta samu wajen inganta kiwon lafiya, ilimi, ayyukan gwamnati da ci gaban tattalin arzikin jihar.
Da yake karɓar lambobin yabon, Gwamna Yusuf ya gode wa ƙungiyoyin da suka karrama shi, yana mai cewa hakan zai ƙara masa ƙwarin gwiwa wajen ci gaba da gudanar da mulki nagari da aiwatar da manufofin da za su amfani al’ummar Kano.










