Ministan Ayyuka na Tarayya, David Umahi, ya yi kira ga masana’antun siminti a Najeriya da su rage farashin kayayyakinsu, yana mai bayyana cewa tsadar siminti na ƙara wa gwamnati nauyin gudanar da ayyukan gine-ginen more rayuwa tare da jinkirta aiwatar da wasu muhimman ayyuka.
Umahi ya bayyana hakan ne a yayin wani taron ƙaddamar da sabon sunan kamfanin Lafarge, wanda yanzu ya koma HBM bayan shiga ƙarƙashin rukunin kamfanonin HUAXIN Group, da aka gudanar a birnin Legas ranar Lahadi.
Ministan ya sanar da cewa gwamnatin tarayya za ta fara tattaunawa da masana’antun siminti daga ranar 1 ga watan Yuli domin nemo hanyoyin rage farashin siminti, wanda ya ce ya zama babban ƙalubale ga masu aiwatar da ayyukan gine-gine a faɗin ƙasar.
Ya ce rage farashin siminti zai taimaka wajen rage kuɗaɗen ayyukan gwamnati da kuma sauƙaƙa wa ’yan ƙasa gina gidaje da sauran muhimman gine-gine.
Haka kuma, ya buƙaci kamfanin HBM dPa sauran masana’antun siminti su ƙara yawan samar da kayayyaki domin biyan buƙatun da ke ƙaruwa, tare da yaba wa masu zuba jari bisa ci gaba da saka hannun jari a tattalin arzikin Najeriya.











