• About
  • Advertise
  • Privacy & Policy
  • Contact
AKSAM
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO
No Result
View All Result
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO
No Result
View All Result
AKSAM
No Result
View All Result

Tinubu Ya Amince da sabbin sauye-sauye a hukumar NYSC, Na Kafa Sabbin Fannonin a hukumar 

Khadija Maitaya by Khadija Maitaya
July 1, 2026
Reading Time: 2 mins read
0
Home LABARAI
ADVERTISEMENT
466
SHARES
1.5k
VIEWS
Share on FacebookShare on Twitter

Shugaban Ƙasa, Bola Tinubu, ya amince da yin cikakken gyara ga tsarin Hukumar Yi wa Ƙasa Hidima (NYSC), inda za a bai wa fararen hula alhakin gudanar da harkokin yau da kullum na hukumar, yayin da jami’an soji za su ci gaba da kula da tsaron masu yi wa ƙasa hidima a faɗin Najeriya.

Fadar Shugaban Ƙasa ta bayyana cewa Tinubu ya umarci Babban Lauyan Tarayya kuma Ministan Shari’a, Lateef Fagbemi, da Ministan Matasa, Ayodele Olawande, da su yi gyaran dokar NYSC domin ta dace da sabbin sauye-sauyen da aka amince da su, tare da ba da damar fara aiwatar da su nan take.

RelatedPosts

Alaqa Na Ƙara Yin Tsami Tsakanin Yariman Saudiyya da Amurka

NUJ Ta Kaddamar da Ƙungiyar Kafafen Yaɗa Labarai na Yanar Gizo a Jihar Jigawa

Iran Ta Ƙera Ƙwaƙwalwar Wucin Gadi Daga Kwayoyin Halittar Ɗan Adam

Daga cikin sauye-sauyen akwai amfani da fasaha wajen kiran masu yi wa ƙasa hidima, tura su zuwa wuraren aiki bisa la’akari da yanayin tsaro, da kuma sake fasalin shirin horaswa na makonni shida.
Haka kuma, an soke faretin kammala bautar ƙasa na gargajiya (Passing Out Parade), inda za a maye gurbinsa da sabon bikin kammala hidima tare da gabatar da sabbin kayan NYSC da za su nuna ƙwarewa da kishin ƙasa.

Mai ba Shugaban Ƙasa shawara ta musamman, Hadiza Bala Usman, ta ce za a raba sansanin horaswar na makonni shida zuwa matakai uku. Makonni na farko da na biyu za su mayar da hankali kan nauyin ɗan ƙasa, ƙimomin ƙasa da haɓaka shugabanci.

A makonni na uku da na huɗu kuma, za a koyar da tsara sana’a, ilimin harkokin kuɗi, dabarun kasuwanci da hanyoyin samun tallafin kuɗi.

Sai makonni na biyar da na shida, waɗanda za a keɓe domin horaswa ta musamman bisa fannin aikin da kowane mai yi wa ƙasa hidima ya zaɓa.

Bugu da ƙari, masu yi wa ƙasa hidima za su riƙa zaɓar ɗaya daga cikin sabbin fannonin horaswa guda 11 yayin yin rajista. Fannonin sun haɗa da: Bangaren Noma, Bangaren Lafiya, Bangaren Ilimi, Bangaren Fasaha da Na’ura Mai Ƙwaƙwalwa, Bangaren Shari’a, Bangaren Ayyukan Gwamnati, Bangaren Ababen More Rayuwa, Bangaren Kare Muhalli, Bangaren Kasuwanci, Bangaren Tattalin Arziki da Ƙirƙira da kuma Bangaren Tsaro.

Hadiza Bala Usman ta bayyana cewa sabbin fannonin za su taimaka wajen bai wa matasa ƙwarewar aiki da ta dace da karatunsu, sha’awarsu ta sana’a da kuma buƙatun ma’aikata a Najeriya, yayin da tura masu yi wa ƙasa hidima zuwa wuraren aiki zai riƙa la’akari da halin tsaro a ƙasar.

Share186Tweet117SendShare
ADVERTISEMENT
Previous Post

NUJ Ta Kaddamar da Ƙungiyar Kafafen Yaɗa Labarai na Yanar Gizo a Jihar Jigawa

Next Post

Alaqa Na Ƙara Yin Tsami Tsakanin Yariman Saudiyya da Amurka

Khadija Maitaya

Khadija Maitaya

RelatedPosts

Alaqa Na Ƙara Yin Tsami Tsakanin Yariman Saudiyya da Amurka
LABARAI

Alaqa Na Ƙara Yin Tsami Tsakanin Yariman Saudiyya da Amurka

by Khadija Maitaya
July 2, 2026
NUJ Ta Kaddamar da Ƙungiyar Kafafen Yaɗa Labarai na Yanar Gizo a Jihar Jigawa
LABARAI

NUJ Ta Kaddamar da Ƙungiyar Kafafen Yaɗa Labarai na Yanar Gizo a Jihar Jigawa

by Khadija Maitaya
July 1, 2026
Iran Ta Ƙera Ƙwaƙwalwar Wucin Gadi Daga Kwayoyin Halittar Ɗan Adam
LABARAI

Iran Ta Ƙera Ƙwaƙwalwar Wucin Gadi Daga Kwayoyin Halittar Ɗan Adam

by Khadija Maitaya
July 1, 2026
Da-dumi-dumi: Iran Ta Yi Barazanar Afkawa Ƙasar Bahrain
LABARAI

Da-dumi-dumi: Iran Ta Yi Barazanar Afkawa Ƙasar Bahrain

by Khadija Maitaya
June 29, 2026

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Recommended.

Bitadakullin siyasa, an yi gidan kaso da sakataren jam’iyar PDP

Bitadakullin siyasa, an yi gidan kaso da sakataren jam’iyar PDP

February 14, 2024
Yanzu-yanzu CBN ya sauke farashin Dalar Amurka warwas

Kungiyar Mata Masu Koyar Da Sana’o’in Hannu Domin Dogaro Da Kai Dake Jihar Kaduna (EDAK), Ta Yaye Dalibain 150 Da Ta Koya Sana’o’i Daban-Daban

June 30, 2024
ADVERTISEMENT

Trending.

Wani Matashi Ya Rasu A Gidan Budurwarsa  ƴar Tik-tok  Dake Unguwar  Ɗanbare A Jihar Kano

Wani Matashi Ya Rasu A Gidan Budurwarsa ƴar Tik-tok Dake Unguwar Ɗanbare A Jihar Kano

June 20, 2026
Mu Na Gayyatar  ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Gurin Daurin Auren:- Ango Bulaye

Mu Na Gayyatar ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Gurin Daurin Auren:- Ango Bulaye

June 12, 2026
Ga Sakon Bangajiya Daga: Angon Sha’ibu Sani Mai Atamfa (Bulaye)

Ga Sakon Bangajiya Daga: Angon Sha’ibu Sani Mai Atamfa (Bulaye)

June 15, 2026
Rundunar  Sojin Najeriya Ta Yi Nasarar Ceto Matar Marigayi Janar Rabe Abubakar Daga Hannun Masu Garkuwa Da Mutane

Rundunar Sojin Najeriya Ta Yi Nasarar Ceto Matar Marigayi Janar Rabe Abubakar Daga Hannun Masu Garkuwa Da Mutane

June 16, 2026
Kungiyar Direbobi ta koka da ƙarancin wuraren Lodi a birnin Kano

Kungiyar Direbobi ta koka da ƙarancin wuraren Lodi a birnin Kano

January 31, 2026

Aksam Hausa

AKSAM MEDIA is a company which designed as online News Platform and other activities related to develop society.

The AKSAM MEDIA created since November 2019 and it does many activities as News publishes it publishes a Hausa News And English News.

No Result
View All Result
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO

© 2023 Aksam media