• About
  • Advertise
  • Privacy & Policy
  • Contact
AKSAM
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO
No Result
View All Result
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO
No Result
View All Result
AKSAM
No Result
View All Result

Shugaban Hukumar Gudanarwar UBRBDA, Barayan Bauchi, Ya Yabawa Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu Kan Ware Naira Tiriliyan 1.2 Da Aka Saka Cikin Bankin Manoman Najeriya

aksam by aksam
August 23, 2025
Reading Time: 3 mins read
0
Home Uncategorized
ADVERTISEMENT
472
SHARES
1.5k
VIEWS
Share on FacebookShare on Twitter

 

 

RelatedPosts

Shekara Kwana: Shekaru 24 Kenan Da Hatsarin Jirgin Sama A Unguwar Gwammaja Dake Jihar Kano

Shirye – Shiryen Fara Jigilar Maniyyata Aikin Hajjin 2026, Na Jihar Kano Ya Kammala

Muna Gayyatar ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Daurin Auren;- UMAR SA’ID

Daga: Hassan Umar Gwammaja

Shugaban Hukumar Gudanarwa na Hukumar Raya Kogin Benue ta Arewa (UBRBDA), wadda ke kula da Jahohin Adamawa, Bauchi, Gombe, da Taraba, Alhaji Sanusi Muhammad Baban Takko (Barayan Bauchi), ya yi yabon da kuma jinjinawa Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu (Jagaban Najeriya) saboda jajircewarsa da ƙwazon da ya nuna wajen farfado da Bankin Manoman Najeriya.

Yayin da yake bayani kan ci gaban, Barayan Bauchi ya bayyana amincewar Naira Tiriliyan 1.2 domin farfado da noman zamani, noman rani, da sauran tsare-tsaren noma a matsayin mataki mai matuƙar muhimmanci wanda zai maido da noma a matsayin ginshiƙin bunƙasar tattalin arzikin Najeriya, musamman Arewacin ƙasar, kamar yadda aka sani a da.

“A matsayina na Shugaban Hukumar Gudanarwa ta Upper Benue River Basin Development Authority, ina mika gaisuwa da goyon baya na gaskiya ga shugaban ƙasarmu mai ƙarfi da basira, Bola Ahmed Tinubu, GCFR, saboda wannan muhimmin mataki da bai taɓa faruwa ba a tarihin ƙasar. Amincewa da wannan babbar adadi na kuɗi zuwa Bankin Manoma na Najeriya domin bashi ga manoma na gaskiya, zai ƙarfafa ci gaban sashen noma, tabbatar da girbin amfanin gona mai yawa, ɗorewar abinci, fitar da kaya zuwa ƙasashen waje, da walwala ga al’umma, har ma da samar da dukiya domin amfanin dukkan ‘yan Najeriya,” in ji shi.

Sai dai Barayan Bauchi, ya roƙi shugabancin Bankin Manoma na Najeriya da su tabbatar da cewa sharuddan karɓar bashin ba su da wahala, yana mai jaddada cewa wannan shi ne kawai hanyar da za a iya cimma burin da muradin mai girma Shugaba Bola Ahmed Tinubu da tawagarsa na ganin Najeriya ta zama ɗaya daga cikin manyan ƙasashen da ke samar da abinci a Afirka, ƙasa da hamadar Sahara da ma duniya baki ɗaya.

Ya ƙara da cewa ƙasashe masu tasowa kamar India da Siri-Lanka sun aiwatar da irin wannan tsari da nasara mai yawa, inda ‘yan ƙasarsu suka more ruwan demokiradiyya ta hanyar wadataccen abinci da bunƙasar noma.

“A wannan dama, ina kiran cibiyoyin gargajiya da sauran masu ruwa da tsaki da su wayar da kan al’ummarmu a ƙarkara a faɗin ƙasa kan wannan sabon tsari na hukuma. Samuwar wadannan kuɗaɗe, Naira Tiriliyan 1.2, da aka saka a cikin Bankin Noma na Najeriya a matsayin bashin ju-yin-ju-ya hali,  na da nufin ba da numfashi ga sashen noma da ya kusa durƙushewa,” in ji Barayan Bauchi.

Shugaban Hukumar UBRBDA ya ƙara tabbatar da cewa, a ƙarƙashin jagorancinsa, hukumar za ta yi aiki kafada da kafada da Bankin Manoma na Najeriya domin ganin cewa Manoman, matasa da manoman rani a jihohin huɗu da ke ƙarƙashin UBRBDA sun ci gajiyar wannan shiri na sauyi da ya fito daga Agenda na Sabon Fata na Shugaba Bola Ahmed Tinubu.

Ya bayyana cewa wannan yana da matuƙar muhimmanci ganin irin matsalolin jinƙai da wannan yanki ya fuskanta sakamakon shekaru na rikice-rikice da sauran ƙalubale.

Har ila yau, Barayan Bauchi ya bukaci Bankin Manoma na Najeriya da ya buɗe ofisoshi a dukkan ƙananan hukumomi 774 na Najeriya, har da yankunan ƙananan hukumomin babban birnin tarayya (FCT), domin buɗe kofofin dama ga manoman gaskiya a ƙarkara, daidai da hangen nesa na shugaban ƙasa na aiki don amfanin kowa da kowa a kowane mataki.

Yayin da yake nuna matuƙar godiyarsa, Barayan Bauchi ya yabawa Shugaba Bola Ahmed Tinubu bisa jajircewarsa wajen gyara manyan sassa na tattalin arzikin ƙasa ta hanyar manyan sauye-sauye tun bayan da ya hau mulki kusan shekaru biyu da suka wuce.

“Mai Girma Shugaban Ƙasa, tarihi da al’umma za su tuna da kai da alheri saboda ƙaddamar da muhimman sauye-sauye da suka shafi magance matsalolin tsaro da abinci da sauran sassan rayuwa. Ina roƙonka da kada ka gaji ko ka karaya a wannan tafiya ta gina ƙasa da kuma gina ƙungiyoyin al’umma da adalci da dai-daito ga kowa da kowa. Kamar yadda ka faɗa, bayan duhu, safiya mai daraja tana zuwa,” in ji shi.

Share189Tweet118SendShare
ADVERTISEMENT
Previous Post

Invitation !!!

Next Post

Kwamitin Fadakar Da Al’umma Mahimmanci Mallakar Katin Zabe Ya Ziyarci Shugaban Hukumar Zabe Na Jihar Kano

aksam

aksam

RelatedPosts

Shekara Kwana: Shekaru 24 Kenan Da Hatsarin Jirgin Sama A Unguwar Gwammaja Dake Jihar Kano
LABARAI

Shekara Kwana: Shekaru 24 Kenan Da Hatsarin Jirgin Sama A Unguwar Gwammaja Dake Jihar Kano

by aksam
May 4, 2026
Shirye – Shiryen Fara Jigilar Maniyyata Aikin Hajjin 2026, Na Jihar Kano Ya Kammala
LABARAI

Shirye – Shiryen Fara Jigilar Maniyyata Aikin Hajjin 2026, Na Jihar Kano Ya Kammala

by aksam
April 17, 2026
Muna Gayyatar ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Daurin Auren;- UMAR SA’ID
Uncategorized

Muna Gayyatar ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Daurin Auren;- UMAR SA’ID

by aksam
April 17, 2026
Araqchi Ya Bukaci Kasashen Duniya Su Dauki Matsaya Ka
Uncategorized

Araqchi Ya Bukaci Kasashen Duniya Su Dauki Matsaya Ka

by aksam
April 11, 2026

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Recommended.

Sheikh Daurawa ya saki sabon gargadi ga masu tambele a TikTok da sauran kafafen sada zumunta

March 5, 2024
Iftila’i: Wani Gini Ya Fado Kan Magina 12 A Jihar Kano

Iftila’i: Wani Gini Ya Fado Kan Magina 12 A Jihar Kano

April 26, 2024
ADVERTISEMENT

Trending.

Mu Na Gayyatar  ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Gurin Daurin Auren:- Comr.  Usaini Sani Adamu !!!

Mu Na Gayyatar ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Gurin Daurin Auren:- Comr. Usaini Sani Adamu !!!

April 24, 2026
Ga Sakon Bangajiya Daga: Angon Umar SA’ID

Ga Sakon Bangajiya Daga: Angon Umar SA’ID

April 20, 2026
Shekara Kwana: Shekaru 24 Kenan Da Hatsarin Jirgin Sama A Unguwar Gwammaja Dake Jihar Kano

Shekara Kwana: Shekaru 24 Kenan Da Hatsarin Jirgin Sama A Unguwar Gwammaja Dake Jihar Kano

May 4, 2026
Muna Gayyatar ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Daurin Auren;- UMAR SA’ID

Muna Gayyatar ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Daurin Auren;- UMAR SA’ID

April 17, 2026
Atiku, Kwankwaso , Obi Sun Jagoranci Zanga-Zanga A Babban Birnin Tarayya Abuja

Atiku, Kwankwaso , Obi Sun Jagoranci Zanga-Zanga A Babban Birnin Tarayya Abuja

April 8, 2026

Aksam Hausa

AKSAM MEDIA is a company which designed as online News Platform and other activities related to develop society.

The AKSAM MEDIA created since November 2019 and it does many activities as News publishes it publishes a Hausa News And English News.

No Result
View All Result
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO

© 2023 Aksam media