Daga: Hassan Umar Gwammaja
Shugaban Hukumar Gudanarwa na Hukumar Raya Kogin Benue ta Arewa (UBRBDA), wadda ke kula da Jahohin Adamawa, Bauchi, Gombe, da Taraba, Alhaji Sanusi Muhammad Baban Takko (Barayan Bauchi), ya yi yabon da kuma jinjinawa Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu (Jagaban Najeriya) saboda jajircewarsa da ƙwazon da ya nuna wajen farfado da Bankin Manoman Najeriya.
Yayin da yake bayani kan ci gaban, Barayan Bauchi ya bayyana amincewar Naira Tiriliyan 1.2 domin farfado da noman zamani, noman rani, da sauran tsare-tsaren noma a matsayin mataki mai matuƙar muhimmanci wanda zai maido da noma a matsayin ginshiƙin bunƙasar tattalin arzikin Najeriya, musamman Arewacin ƙasar, kamar yadda aka sani a da.
“A matsayina na Shugaban Hukumar Gudanarwa ta Upper Benue River Basin Development Authority, ina mika gaisuwa da goyon baya na gaskiya ga shugaban ƙasarmu mai ƙarfi da basira, Bola Ahmed Tinubu, GCFR, saboda wannan muhimmin mataki da bai taɓa faruwa ba a tarihin ƙasar. Amincewa da wannan babbar adadi na kuɗi zuwa Bankin Manoma na Najeriya domin bashi ga manoma na gaskiya, zai ƙarfafa ci gaban sashen noma, tabbatar da girbin amfanin gona mai yawa, ɗorewar abinci, fitar da kaya zuwa ƙasashen waje, da walwala ga al’umma, har ma da samar da dukiya domin amfanin dukkan ‘yan Najeriya,” in ji shi.
Sai dai Barayan Bauchi, ya roƙi shugabancin Bankin Manoma na Najeriya da su tabbatar da cewa sharuddan karɓar bashin ba su da wahala, yana mai jaddada cewa wannan shi ne kawai hanyar da za a iya cimma burin da muradin mai girma Shugaba Bola Ahmed Tinubu da tawagarsa na ganin Najeriya ta zama ɗaya daga cikin manyan ƙasashen da ke samar da abinci a Afirka, ƙasa da hamadar Sahara da ma duniya baki ɗaya.
Ya ƙara da cewa ƙasashe masu tasowa kamar India da Siri-Lanka sun aiwatar da irin wannan tsari da nasara mai yawa, inda ‘yan ƙasarsu suka more ruwan demokiradiyya ta hanyar wadataccen abinci da bunƙasar noma.
“A wannan dama, ina kiran cibiyoyin gargajiya da sauran masu ruwa da tsaki da su wayar da kan al’ummarmu a ƙarkara a faɗin ƙasa kan wannan sabon tsari na hukuma. Samuwar wadannan kuɗaɗe, Naira Tiriliyan 1.2, da aka saka a cikin Bankin Noma na Najeriya a matsayin bashin ju-yin-ju-ya hali, na da nufin ba da numfashi ga sashen noma da ya kusa durƙushewa,” in ji Barayan Bauchi.
Shugaban Hukumar UBRBDA ya ƙara tabbatar da cewa, a ƙarƙashin jagorancinsa, hukumar za ta yi aiki kafada da kafada da Bankin Manoma na Najeriya domin ganin cewa Manoman, matasa da manoman rani a jihohin huɗu da ke ƙarƙashin UBRBDA sun ci gajiyar wannan shiri na sauyi da ya fito daga Agenda na Sabon Fata na Shugaba Bola Ahmed Tinubu.
Ya bayyana cewa wannan yana da matuƙar muhimmanci ganin irin matsalolin jinƙai da wannan yanki ya fuskanta sakamakon shekaru na rikice-rikice da sauran ƙalubale.
Har ila yau, Barayan Bauchi ya bukaci Bankin Manoma na Najeriya da ya buɗe ofisoshi a dukkan ƙananan hukumomi 774 na Najeriya, har da yankunan ƙananan hukumomin babban birnin tarayya (FCT), domin buɗe kofofin dama ga manoman gaskiya a ƙarkara, daidai da hangen nesa na shugaban ƙasa na aiki don amfanin kowa da kowa a kowane mataki.
Yayin da yake nuna matuƙar godiyarsa, Barayan Bauchi ya yabawa Shugaba Bola Ahmed Tinubu bisa jajircewarsa wajen gyara manyan sassa na tattalin arzikin ƙasa ta hanyar manyan sauye-sauye tun bayan da ya hau mulki kusan shekaru biyu da suka wuce.
“Mai Girma Shugaban Ƙasa, tarihi da al’umma za su tuna da kai da alheri saboda ƙaddamar da muhimman sauye-sauye da suka shafi magance matsalolin tsaro da abinci da sauran sassan rayuwa. Ina roƙonka da kada ka gaji ko ka karaya a wannan tafiya ta gina ƙasa da kuma gina ƙungiyoyin al’umma da adalci da dai-daito ga kowa da kowa. Kamar yadda ka faɗa, bayan duhu, safiya mai daraja tana zuwa,” in ji shi.











