• About
  • Advertise
  • Privacy & Policy
  • Contact
AKSAM
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO
No Result
View All Result
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO
No Result
View All Result
AKSAM
No Result
View All Result

Sheikh Daurawa ya saki sabon gargadi ga masu tambele a TikTok da sauran kafafen sada zumunta

aksam by aksam
March 5, 2024
Reading Time: 2 mins read
0
Home LABARAI
ADVERTISEMENT
470
SHARES
1.5k
VIEWS
Share on FacebookShare on Twitter

Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa ya ba da wa’adin sati biyu Dan jankunne ga marasa da’a dake gudanar da tambele a kafafen sada zumunta na zamani wato social media a turance.

Daurawa ya  bayar da wa’adin ne jim kaɗan bayan dawowa kan mukaminsa, bayan samun fahimtar juna da gwamna Abba Kabir Yusuf.

RelatedPosts

Sarkin Zurmi Ya Rasu Bayan Shekaru Biyar A Kan Sarauta

Kano State Govt ends 50 year BUK/Rimin zakara Land Dispute

Yaki da harkar Daba a Jihar Kano

Cikin sakon da hukumar ta wallafa a shafinta na Facebook mai taken jan kunne, Sheikh Aminu Daurawa yace da bata-garin, “Sati biyu kacal na baku ku tuba ko Hisbah ta murƙushe ku.”

A daren Litinin 4/3/2024 aka sasanta Sheikh Daurawa da Gwamna Abba a wani zama da Majalisar Haɗin Kan Malamai da Ƙungiyoyin Jihar Kano ta jagoranta a gidan gwamnatin jihar.

Majiya mai tushe ta shaida cewa Babban Limamin Masallacin ƙasa da ke Abuja, Sheikh Ibrahim Maƙari da Shugaban Majalisar Dokokin Jihar Kano, Jibril Falgore, suna daga cikin waɗanda Gwamna Abba ya turo domin su yi masa bikon Sheikh Daurawa.

Murabus din Sheikh Daurawa daga shugabancin Hisbah dai ya bar baya da ƙura, inda aka yi ta kiraye-kiraye da roƙon sa ya koma ya dora a kan nasarorin da hukumar ta samu a ƙarkashin jagorancinsa, musamman a ɓangaren yaƙi da badala.

A Juma’ar da Sheikh Daurawa ya sauka, wasu ƴan daudu sun kai wa jami’an Hisbah hari a ofishinsu a Kano, baya ga wata dabdala da suka gudanar tare da mata masu zaman kansu domin murnar saukar malamin.

Tun ranar Alhamis a lokacin taron da Gwamna Abba ya yi da malaman Jihar Kano kan shirye-shiryen azumin Ramadan da ke tafe ne gwamnan ya soki yadda jami’an Hisbah ke kai samame a matattaran bata-gari suna yi wa bata-garin ɗiban karan mahaukaciya, ba maza, ba mata, ake ta ce-ce-ku-ce.
Wasu dai na ganin gwamnan ya yi daidai domin gyara ne ya yi wa hukumar ayyukanta, saboda jami’anta suna wuce gona da iri.

A gefe guda kuma wasu na ganin gwamnan ya yi katobara, kuma kalaman nasa tamkar kariya ce ga masu ayyukan masha’a a jihar, da kuma fifita su a kan malamin, wanda suke ganin an ci mutuncinsa, musamman ganin cewa malamin ba ya wurin kuma gwamnan na da ikon kiran sa ya yi masa gyara ba a bainar jama’a ba.

Hasali ma tun watanni uku da suka wuce da abin ya faru Sheikh Daurawa ya sanar cewa sun gyara kuskuren, har sun hukunta waɗanda suka aikata ba daidai ba.

Washegari, Juma’a da sassafe Sheikh Daurawa ya sanar cewa ya sauka da muƙamin, saboda kalaman gwamnan, sannan ya yi wa gwamnan da gwamnatinsa  fatan alheri da samun nasara, matakin da wasu ke ganin ya yi daidai.

Wasu dai na zargin subul-da-bakan gwamnan ya yi na da alaka da dambarwar shahararriyar ƴan tiktok Murja Kunya, wadda ta tayar da ƙura bayan an fitar da ita daga gidan yarin da kotu ta ba da umarnin ta bayan hukumar Hisbah ta gurfanar da ita kan zargin lalata tarbiyya tare da koya wa yara karuwanci da kuma razana jama’a.

Da dama daga cikin jama’a na zargin akwai hannun gwamnatin jihar Kano wajen fitar da Murja daga gidan yarin ta barauniyar hanya, zargin da gwamnatin ta musanta.

Share188Tweet118SendShare
ADVERTISEMENT
Previous Post

Wani gwamna yayi tanadin wutar lantarki na wata guda babu daukewa ga yan jihar sa

Next Post

Hukumar Karbar Korafe-Korafe, Da Yaki Da Cin Hanci Da Rashawa Ta Jihar Kano Ba Da Hurin Bicikar Fefan Video Dollar Ganduje:- Kotu

aksam

aksam

RelatedPosts

Sarkin Zurmi Ya Rasu Bayan Shekaru Biyar A Kan Sarauta
LABARAI

Sarkin Zurmi Ya Rasu Bayan Shekaru Biyar A Kan Sarauta

by Khadija Maitaya
September 1, 2026
Kano State Govt ends 50 year BUK/Rimin zakara Land Dispute
LABARAI

Kano State Govt ends 50 year BUK/Rimin zakara Land Dispute

by Khadija Maitaya
August 31, 2026
Gwamnatin Kano Ta Jaddada Haɗin Gwiwa Tsakanin Kafafen Yaɗa Labarai da Hukumomin Tsaro
LABARAI

Yaki da harkar Daba a Jihar Kano

by Khadija Maitaya
August 31, 2026
Babban Malami Ya Kalubalanci Gwamnoni da ’Yan Majalisa Bisa Rufe Cibiyoyi 10 Na Yin Fasfo
LABARAI

Babban Malami Ya Kalubalanci Gwamnoni da ’Yan Majalisa Bisa Rufe Cibiyoyi 10 Na Yin Fasfo

by Khadija Maitaya
August 30, 2026

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Recommended.

Die Rolle von RNG in n1bet casino Spielen

April 22, 2025
Yaƙi da Rashin tarbiyya, Gwamnan Niger ya saka dokoki 10 masu zafi ga yan siyasa da masu siyar da Kayan maye

Yaƙi da Rashin tarbiyya, Gwamnan Niger ya saka dokoki 10 masu zafi ga yan siyasa da masu siyar da Kayan maye

April 23, 2025
ADVERTISEMENT

Trending.

Masu Siye Da Siyar Da Filaye A  R/zakara Sunkoka Da Aibantasu Da Gwamnatin Kano Keyi.

Masu Siye Da Siyar Da Filaye A  R/zakara Sunkoka Da Aibantasu Da Gwamnatin Kano Keyi.

August 26, 2026
Cristiano Ronaldo Ya Auri Georgina Rodríguez

Cristiano Ronaldo Ya Auri Georgina Rodríguez

August 12, 2026
Wani Kauran Mata Ya Jikkata Wata Dattijuwa Bayan Ta Hana Shi Shiga Gurin Da Bai kamata Ba

Wani Kauran Mata Ya Jikkata Wata Dattijuwa Bayan Ta Hana Shi Shiga Gurin Da Bai kamata Ba

August 29, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Matar Aure Hukunci Bayan Samunta Da Watsa Tafasasshen Ruwa Ga Kishiyarta

Kotu Ta Yanke Wa Matar Aure Hukunci Bayan Samunta Da Watsa Tafasasshen Ruwa Ga Kishiyarta

August 7, 2026
Iran Ta Kakkabo Wasu Manyan Jiragen Yaƙi Na Amurka

Iran Ta Kakkabo Wasu Manyan Jiragen Yaƙi Na Amurka

August 14, 2026

Aksam Hausa

AKSAM MEDIA is a company which designed as online News Platform and other activities related to develop society.

The AKSAM MEDIA created since November 2019 and it does many activities as News publishes it publishes a Hausa News And English News.

No Result
View All Result
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO

© 2023 Aksam media