• About
  • Advertise
  • Privacy & Policy
  • Contact
AKSAM
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO
No Result
View All Result
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO
No Result
View All Result
AKSAM
No Result
View All Result

Dalilan Ayya­na Zaɓen Cike Gurbi A Jihar Zamfara A Matsayin Wanda Bai Kammala Ba —INEC

aksam by aksam
August 17, 2025
Reading Time: 2 mins read
0
Home Uncategorized
ADVERTISEMENT
466
SHARES
1.5k
VIEWS
Share on FacebookShare on Twitter

RelatedPosts

Shekara Kwana: Shekaru 24 Kenan Da Hatsarin Jirgin Sama A Unguwar Gwammaja Dake Jihar Kano

Shirye – Shiryen Fara Jigilar Maniyyata Aikin Hajjin 2026, Na Jihar Kano Ya Kammala

Muna Gayyatar ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Daurin Auren;- UMAR SA’ID

Daga Hassan Umar Gwammaja

Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC) ta bayyana cewa zaɓen cike gurbi na majalisar wakilai a mazaɓar Kaura Namoda ta Kudu a jihar Zamfara bai kammala ba saboda dalilai na doka da kuma adadin katin zaɓe da ke hannun masu kada kuri’a.

Baturen zaɓen mazaɓar, Lawal Sa’adu daga Jami’ar Tarayya da ke Gusau, ne ya bayyana haka a lokacin da yake sanar da soke sakamakon rumfunan zaɓe na Sakajiki da Kambarawa.

 

Ya ce a wuraren da abin ya shafa an yi rajistar katin zaɓe 5,446, amma adadin masu katin da ke hannun jama’a bai wuce 3,265 ba.

A cewar sa, jam’iyyar APC ta samu ƙuri’u 7,001, yayin da PDP ta samu ƙuri’u 5,339, inda ake da ratar ƙuri’u 1,662. Sai dai ya ce wannan ratar ta yi ƙasa da adadin katin da ke hannun masu zaɓa a rumfunan da aka soke, abin da ya sanya zaɓen ya kasance wanda bai kammala ba.

Hukumar zaɓen ta kafa hujja da dokar zaɓe ta 2022, musamman sashe na 24 (2 & 3), sashe na 47 (3) da kuma sashe na 51 (2), wacce ta tanadi cewa zaɓe zai kasance bai kammala ba idan ratar ƙuri’un da mai nasara ya samu ba ta haura adadin katin da ke hannun jama’a

 

Sakajiki: Rumfunan zaɓe biyu, inda aka yi rajistar 1,357, masu katin a hannu 1,298.

Kambarawa: Rumfunan zaɓe uku, inda aka yi rajistar 4,088, masu katin a hannu 1,964.

Sa’adu ya bayyana cewa zaɓen zai ci gaba da kasancewa a matsayin wanda bai kammala ba har sai an sake gudanar da zaɓe a waɗannan wurare.

INEC ta ce za ta sanar da ranar da za a sake gudanar da zaɓe a Sakajiki da Kambarawa a wani lokaci nan gaba

 

Share186Tweet117SendShare
ADVERTISEMENT
Previous Post

Yunkurin dukan mahaifiya, Kotu ta yanke zaman shekara daya a gidan kaso ga wani matashi

Next Post

Adam A Zango Ya Auri Wata ‘Yar Fim A Sirrince

aksam

aksam

RelatedPosts

Shekara Kwana: Shekaru 24 Kenan Da Hatsarin Jirgin Sama A Unguwar Gwammaja Dake Jihar Kano
LABARAI

Shekara Kwana: Shekaru 24 Kenan Da Hatsarin Jirgin Sama A Unguwar Gwammaja Dake Jihar Kano

by aksam
May 4, 2026
Shirye – Shiryen Fara Jigilar Maniyyata Aikin Hajjin 2026, Na Jihar Kano Ya Kammala
LABARAI

Shirye – Shiryen Fara Jigilar Maniyyata Aikin Hajjin 2026, Na Jihar Kano Ya Kammala

by aksam
April 17, 2026
Muna Gayyatar ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Daurin Auren;- UMAR SA’ID
Uncategorized

Muna Gayyatar ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Daurin Auren;- UMAR SA’ID

by aksam
April 17, 2026
Araqchi Ya Bukaci Kasashen Duniya Su Dauki Matsaya Ka
Uncategorized

Araqchi Ya Bukaci Kasashen Duniya Su Dauki Matsaya Ka

by aksam
April 11, 2026

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Recommended.

Yadda Yan kasuwar kayayyakin gona ke kokawa da farashin man fetur

Yadda Yan kasuwar kayayyakin gona ke kokawa da farashin man fetur

September 28, 2023
Sha’anin tsaro, Atiku ya tambayi Tinubu Abu mai rikitarwa

Sha’anin tsaro, Atiku ya tambayi Tinubu Abu mai rikitarwa

July 8, 2024
ADVERTISEMENT

Trending.

Mu Na Gayyatar  ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Gurin Daurin Auren:- Comr.  Usaini Sani Adamu !!!

Mu Na Gayyatar ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Gurin Daurin Auren:- Comr. Usaini Sani Adamu !!!

April 24, 2026
Ga Sakon Bangajiya Daga: Angon Umar SA’ID

Ga Sakon Bangajiya Daga: Angon Umar SA’ID

April 20, 2026
Shekara Kwana: Shekaru 24 Kenan Da Hatsarin Jirgin Sama A Unguwar Gwammaja Dake Jihar Kano

Shekara Kwana: Shekaru 24 Kenan Da Hatsarin Jirgin Sama A Unguwar Gwammaja Dake Jihar Kano

May 4, 2026
Muna Gayyatar ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Daurin Auren;- UMAR SA’ID

Muna Gayyatar ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Daurin Auren;- UMAR SA’ID

April 17, 2026
Atiku, Kwankwaso , Obi Sun Jagoranci Zanga-Zanga A Babban Birnin Tarayya Abuja

Atiku, Kwankwaso , Obi Sun Jagoranci Zanga-Zanga A Babban Birnin Tarayya Abuja

April 8, 2026

Aksam Hausa

AKSAM MEDIA is a company which designed as online News Platform and other activities related to develop society.

The AKSAM MEDIA created since November 2019 and it does many activities as News publishes it publishes a Hausa News And English News.

No Result
View All Result
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO

© 2023 Aksam media