A wata sanarwa da kakakin rundunar, SP Abdullahi Haruna Kiyawa, ya fitar, ya ce an kama wadanda ake zargin ne tsakanin 23 zuwa 28 ga Afrilu, 2025, bayan samun bayanan sirri daga jama’a.
Sanarwar ta ce tawagar musamman da CSP Bashir Musa Gwadabe ke jagoranta ta cafke mutanen dauke da makamai masu hadari, miyagun kwayoyi da kayan sata.
Kwamishinan ’Yan Sanda na Kano, CP Ibrahim Adamu Bakori, ya bayyana cewa, rundunar za ta ci gaba da gudanar da sintiri da samame don tabbatar da zaman lafiya, tare da karfafa hulda da al’umma domin dakile miyagun ayyuka.
Kwamishinan ya yaba wa hadin kan jama’a tare da bukatar su ci gaba da bai wa ’yan sanda bayanan sirri don taimakawa wajen yaki da laifuka.











