Shugaban Nageriya, Bola Ahmed Tinubu ya bayyana sunan Dr. Olayemi Michael Cardoso a matsayin sabon gwamnan Babban Bankin kasar (CBN) na tsawon shekara biyar.
Shugaban ya tura Majalisar Dattijan ƙasar domin neman amincewa da shi.
Bayani na ƙunshe ne cikin wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban ƙasar, Ajuri Ngelale ya fitar, a yau Juma’a.
Bayanin ya ce shugaban ya ɗauki matakin ne bisa dogaro da sashe na 8 (1) na dokar Babban Bankin Najeriya ta 2007, wadda ta bai wa shugaban ƙasa karfin m na naɗa shugaba da mataimaka huɗu na Babban Bankin.
Wadanda shugaban ya amince da su a matsayin mataimakan gwamnan babban bankin sun hadar da:
Dr. Bala M. Bello
Mr. Muhammad Sani Abdullahi Dattijo
Mrs. Emem Nnana Usoro
Mr. Philip Ikeazor












