Daga ƙarshen makon da ya gabata zuwa farkon wannan mako, an riƙa yaɗa wani faifan bidiyo a kasar nan cikin harshen Hausa, wanda a ciki ake iya ganin wani jami’in sojin Najeriya tare da wani soja farar fata a bayansa.
Masu yaɗa bidiyon sun bayyana cewa baturen da ke cikin bidiyon ɗaya ne daga cikin sojojin Faransa da suka isa jihar Borno da ke Najeriya domin taimaka wa sojin Najeriya wajen yaƙi da mayaƙan Boko Haram.
Borno jiha ce da ta kasance cibiyar rikicin Boko Haram, ƙungiya da ta shafe sama da shekara 10 tana kai hare-hare kan jami’an tsaro da farar hula a yankin arewa maso Gabas na kasar nan .
Rikicin wanda ya shafi ƙasashe masu maƙwaftaka, kamar Jamhuriyar Nijar, da Chadi da kuma Kamaru ya yi sanadin rasa rayukan mutum aƙalla 36,000 da kuma tarwatsa wasu mutanen fiye da miliyan ɗaya.
Duk da cewa sojojin Najeriya sun samu nasarar rage kaifin hare-haren ƙungiyar, har ma a baya hukumomi suka ayyana ‘yin galaba’ a kanta, har yanzu mayaƙan ƙungiyar na kai hare-hare lokaci zuwa lokaci.
Ba dai sabon abu ba ne a ga ƙasashen da ke fama da irin waɗannan rikice-rikice na samun taimakon ƙasashen duniya a ƙoƙarin daƙile irin waɗannan ayyuka na masu ƙungiyoyin masu tayar da tarzoma.
Shi ya sanya kafin yanzu, wasu daga cikin ƙasashen yammacin Afirka da na Sahel suka bai wa manyan ƙasashen duniya damar kafa sansanonin soji a cikinsu da sunan yaƙi da ayyukan ta’addanci a yankin.
Sai dai bayan juyin mulki a Jamhuriyar Nijar da Mali da kuma Burkin Faso, ƙasashen uku sun raba gari da uwargijiyarsu Faransa da kuma Amurka da ma wasu ƙasashen Turai, ta hanyar katse yarjejeniyoyi na tsaro da su.
To amma mece ce gaskiyar bidiyon da ake yaɗawa na cewa sojojin Faransa sun isa Najeriya a wani yunƙuri na kafa sansani?
A tattaunawarsa da manema labarai, daraktan yaɗa labarai na shalkwatar tsaro ta Najeriya, Birgediya-Janar Tukur Gusau ya musanta batun isar tawagar sojin Faransa Najeriya.
Ya ce “idan za a iya tunawa, tun kafin ma a saki wannan bidiyo, CDS (Babban hafsan sojin Najeriya) ya faɗi cewa babu wata yarjejeniya domin kawo sojojin Faranshi a kowane yanki na faɗin Najeriya”.
Janar Gusau ya bayyana cewa bidiyon da ake yaɗawa tsoho ne kuma ba sojojin Faransa ba ne a cikin bidiyon.
Tun farko, shalkwatar tsaro ta Najeriya ta fitar da wata sanarwa da safiyar ranar Litinin tana musanta kasancewar sojin na Faransa a Najeriya.
Sanarwar, wadda ta samu sa hannu daraktan kula da sashen yaɗa labaru na shalkwatar tsaron, Manjo-Janar Edward Buba, ta ce “an janyo hankalinta kan wasu rahotanni da ake yaɗawa a shafukan intanet da ke cewa wata tawagar sojin Faransa ta isa Maiduguri a wani yunƙuri na kafa sansanin sojin Faransa a arewa maso yammacin Najeriya”.
“Wannan bayani ƙage ne, ƙarya ce kuma an yi ne da wata manufa,” kamar yadda sanarwar ta bayyana.











