• About
  • Advertise
  • Privacy & Policy
  • Contact
AKSAM
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO
No Result
View All Result
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO
No Result
View All Result
AKSAM
No Result
View All Result

Kwamishinonin El-Rufa’i sun magantu game almundahnar da ake zargin gwamnatinsa ta yi

aksam by aksam
July 10, 2024
Reading Time: 1 min read
0
Home LABARAI
ADVERTISEMENT
466
SHARES
1.5k
VIEWS
Share on FacebookShare on Twitter

Tsofaffin kwamishinoni takwas na Kaduna sun yi karin haske kan rahoton majalisar jihar da ya zargi tsohuwar gwamnati da almundahana

Tsofaffin mukarraban gwamnatin sun karyata rahoton majalisar da ya ce gwamnatin El-Rufai ta karkatar da Naira biliyan 423

RelatedPosts

Gwamnan Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf Ya Sanya Ranar Talata 05 GA watan Mayu 2026, A Matsayin Ranar Da Zai Jagoranci Rantsar Da Murtala Sule Garo A Matsayin Mataimakin Gwamnan

Shekara Kwana: Shekaru 24 Kenan Da Hatsarin Jirgin Sama A Unguwar Gwammaja Dake Jihar Kano

NDLEA Ta Kama Mutane 6, Ta Rushe Maboyar Miyagun Kwayoyi a BUK Old Site Kano

Hakazalika tsofaffin kwamishinonin sun ce akwai basussukan da gwamnatin El-Rufai ta nemo amma gwamnatin Uba Sani ce ta karbi kudin

A zantawarsu da manema labarai a Abuja, a ranar Talata, tsofaffin kwamishinoni takwas na gwamnatin El-Rufai sun karyata zarge-zargen majalisar Kaduna, inji rahoton Leadership.

Tsofaffin jami’an sun yi watsi da zargin da ake yi wa gwamnatin El-Rufai na cewa ita ce ta karbo dukkanin basussukan da suka yi wa jihar katutu a yanzukafin ta bar ofis a Mayun 2023.

Sun kuma bayyana zargin da majalisar dokokin Kaduna ta yi na cewa tsohuwar gwamnatin ta karkatar da kudaden jihar N423bn a matsayin rashin adalci.

Tsofaffin kwamishinonin da suka yi magana da manema labarai sun hada da Jafaru Sani (ma’aikatar muhalli da ilimi), Hafsat Baba (ma’aikatar jin dadi da bunkasa jama’a) da Thomas Gyang (ma’aikatar ayyukan, da tsare-tsare da kasafin kudi).

Sauran sun hada da: Bashir Saidu (ma’aikatar kudi); Ibrahim Husaini (ma’aikatar noma da muhalli), Aisha Dikko (ma’aikatar shari’a), Fausat Ibikunle (ma’aikatar gidaje da raya birane), da Idris Nyam (ma’aikatar kasuwanci, da kirkira da fasaha).

Sun bayyana tuhumar da majalisar ta yi a matsayin kamfe na batanci ga tsohon gwamnan, inda suka bayyana cewa rahoton ya dogara ne da wasu alkaluma da aka gina su akan karya.

Tags: Aksam radioaminiyaArewa radioBbchausaDAILY TRUSTfreedom radioKadaura24SamoaSolacebasetrthausavoahausa
Share186Tweet117SendShare
ADVERTISEMENT
Previous Post

Bayan sanar da Bude Boda, kalli yadda farashin kayan abinci ya fara rage kudade masu yawa

Next Post

Gwamna Umara Zulum ya yaye karin tubabbun ya Boko Haram 560

aksam

aksam

RelatedPosts

Gwamnan Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf Ya Sanya Ranar Talata 05 GA watan Mayu 2026, A Matsayin Ranar Da Zai Jagoranci Rantsar Da Murtala Sule Garo A Matsayin Mataimakin Gwamnan
LABARAI

Gwamnan Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf Ya Sanya Ranar Talata 05 GA watan Mayu 2026, A Matsayin Ranar Da Zai Jagoranci Rantsar Da Murtala Sule Garo A Matsayin Mataimakin Gwamnan

by aksam
May 4, 2026
Shekara Kwana: Shekaru 24 Kenan Da Hatsarin Jirgin Sama A Unguwar Gwammaja Dake Jihar Kano
LABARAI

Shekara Kwana: Shekaru 24 Kenan Da Hatsarin Jirgin Sama A Unguwar Gwammaja Dake Jihar Kano

by aksam
May 4, 2026
NDLEA Ta Kama Mutane 6, Ta Rushe Maboyar Miyagun Kwayoyi a BUK Old Site Kano
LABARAI

NDLEA Ta Kama Mutane 6, Ta Rushe Maboyar Miyagun Kwayoyi a BUK Old Site Kano

by Khadija Maitaya
May 4, 2026
Tsohon Dan Takarar Shugaban Kasa A  Jam’iyyar Labour Party, Peter Obi, Ya Sanar Da Ficewarsa Daga  Jam’iyyar Haɗaka Ya ADC
LABARAI

Tsohon Dan Takarar Shugaban Kasa A Jam’iyyar Labour Party, Peter Obi, Ya Sanar Da Ficewarsa Daga Jam’iyyar Haɗaka Ya ADC

by aksam
May 3, 2026

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Recommended.

Sabon Mai Baiwa Gwamnan Kano Shawara Kan Ayyuka, Injiniya Ahmad Ishaq Bunkure Ya Rasu, Kwana Daya Da Gwamna Abba Kabir Yusuf Ya Rantsar Da Shi a Gidan Gwamnati.

Sabon Mai Baiwa Gwamnan Kano Shawara Kan Ayyuka, Injiniya Ahmad Ishaq Bunkure Ya Rasu, Kwana Daya Da Gwamna Abba Kabir Yusuf Ya Rantsar Da Shi a Gidan Gwamnati.

January 8, 2025
Yadda India wa ke sa rai da jawabin FM Modi a ranar ruwa ta India

Yadda India wa ke sa rai da jawabin FM Modi a ranar ruwa ta India

October 28, 2025
ADVERTISEMENT

Trending.

Shekara Kwana: Shekaru 24 Kenan Da Hatsarin Jirgin Sama A Unguwar Gwammaja Dake Jihar Kano

Shekara Kwana: Shekaru 24 Kenan Da Hatsarin Jirgin Sama A Unguwar Gwammaja Dake Jihar Kano

May 4, 2026
Mu Na Gayyatar  ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Gurin Daurin Auren:- Comr.  Usaini Sani Adamu !!!

Mu Na Gayyatar ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Gurin Daurin Auren:- Comr. Usaini Sani Adamu !!!

April 24, 2026
Ga Sakon Bangajiya Daga: Angon Umar SA’ID

Ga Sakon Bangajiya Daga: Angon Umar SA’ID

April 20, 2026
Muna Gayyatar ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Daurin Auren;- UMAR SA’ID

Muna Gayyatar ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Daurin Auren;- UMAR SA’ID

April 17, 2026
Atiku, Kwankwaso , Obi Sun Jagoranci Zanga-Zanga A Babban Birnin Tarayya Abuja

Atiku, Kwankwaso , Obi Sun Jagoranci Zanga-Zanga A Babban Birnin Tarayya Abuja

April 8, 2026

Aksam Hausa

AKSAM MEDIA is a company which designed as online News Platform and other activities related to develop society.

The AKSAM MEDIA created since November 2019 and it does many activities as News publishes it publishes a Hausa News And English News.

No Result
View All Result
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO

© 2023 Aksam media