Kungiyar malaman jami’o’i ta kasa (ASUU) ta ba gwamnatin shugaba Bola Tinubu wa’adin makonni biyu domin biya mata bukatun ta ko ta tsunduma yajin aiki.
A jiya Talata ne shugaba kungiyar, Farfesa Emmanuel Osodeke ya bayyana wa manema labarai matakin da suka dauka.
Jaridar Punch ta ruwaito shugaban yana cewa sun ba gwamantin Bola Tinubu wadataccen lokaci da za ta magance matsalolinsu amma ta gagara taɓuka komai.
Har ila yau shugaban kungiyar ya ce majalisar zartarwar kungiyar za ta zauna domin kara kallon lamarin.
A cewarsa majalisar zartarwar ta lura da cewa gwamnatin ta nuna halin ko in kula kan matsalolin kungiyar saboda haka dole su dauki mataki, rahoton Business Day.
Manyan bukatun kungiyar ASUU guda 9
1. Farkon abin da ASUU ta zargi gwamnatin Tinubu da shi shine rashin bada kofa domin cigaba da tattaunawa kan yarjejeniyar da suka yi da gwamnati a 2009 (2009 FGN/ASUU Agreement).
Yarjejeniyar za ta bada dama wurin samun walwala ne ga malaman jami’a domin yin aiki cikin tsari.
2. Abu na biyu shine rusa tsarin majalisun gudanar da jami’o’i da shugaba Tinubu ya yi a watan Yunin 2023.
Kungiyar ta ce rusa majalisun ya saɓa dokar kasa kuma ya haifar da giɓi babba a aikin jami’a a Najeriya.
3. Abu na gaba da kungiyar ASUU ta zargi gwamnatin a kai shine cigaba da biyan malaman jami’a albashi ta manhajar IPPIS.
Duk da cewa Bola Tinubu ya ce an cire malaman jami’o’i a tsarin tun watan Disambar bara amma kungiyar ta ce babu abin da ya canja.
4. Lamarin na hudu da zai iya jefa kungiyar yajin aiki shine fitar da sabon tsarin karatun jami’a a Najeriya.
Kungiyar ta yi watsi da sabon tsarin da gwamnati ta fitar na karatun jami’a duk da cewa gwamnatin na kokarin tilasta aiki da shi.
5. Yawaitar jami’o’in gwamnati a Najeriya shine abu na biyar da kungiyar ta koka ga gwamnatin Bola Tinubu.
Kungiyar ta ce maimakon inganta jami’o’in da ake dasu gwamantin ta dukufa wurin samar da sababbin jami’o’in da ba za ta iya daukan nauyinsu yadda ya kamata ba.
6. Abu na shida da ake dambarwa a kai shine cigaba da ɗaukan dawainiyar jami’o’i yadda ya kamata.
Kungiyar ASUU ta zargi gwamnatin tarayya da kokarin karkatar da kudaden da hukumar TETFund ke amfani da su wajen raya jami’o’i zuwa harkokin lamunin dalibai.
7. Korar ma’aikatan jami’a ba bisa ka’ida ba shine abu na bakwai da kungiyar ASUU ta ke kalubalantar gwamantin Tinubu.
Kungiyar ta ce tana da rahotanni a kan yadda ake wulakanta jami’anta a jami’ar Lagos da jami’ar Kogi da jami’ar fasaha da ke Owerri.
8. Abu na takwas da kungiyar ASUU ta koka shine yadda gwamnatin to tsohe kunnuwa kan alawus da ya kamata ta biya ta.
Gwamnatin ta gaza saka kudin alawus din da kungiyar ke binta a cikin kasafin kudin shekarar 2023.
9. A karshe kungiyar ta koka kan yadda lamura suka tabarbare a Najeriya da yadda talakawa ke kara shiga kuncin rayuwa.
A cewar kungiyar, dole gwamantin Bola Tinubu ta nemo mafita domin saukaka rayuwar al’ummar Najeriya.












