• About
  • Advertise
  • Privacy & Policy
  • Contact
AKSAM
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO
No Result
View All Result
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO
No Result
View All Result
AKSAM
No Result
View All Result

Baya ga barazanar tafiya yajin aiki ASUU ta ambaci wasu manyan abubuwa tara

aksam by aksam
May 15, 2024
Reading Time: 2 mins read
0
Home LABARAI
ADVERTISEMENT
466
SHARES
1.5k
VIEWS
Share on FacebookShare on Twitter

Kungiyar malaman jami’o’i ta kasa (ASUU) ta ba gwamnatin shugaba Bola Tinubu wa’adin makonni biyu domin biya mata bukatun ta ko ta tsunduma yajin aiki.

A jiya Talata ne shugaba kungiyar, Farfesa Emmanuel Osodeke ya bayyana wa manema labarai matakin da suka dauka.

RelatedPosts

Wani Matashi Ya Rasu A Gidan Budurwarsa ƴar Tik-tok Dake Unguwar Ɗanbare A Jihar Kano

Gwamnatin Kano Ta Jaddada Haɗin Gwiwa Tsakanin Kafafen Yaɗa Labarai da Hukumomin Tsaro

Sky News: Yaƙin Trump da Iran Na Daya Daga Cikin Manyan Kurakuran Dabarun Amurka

Jaridar Punch ta ruwaito shugaban yana cewa sun ba gwamantin Bola Tinubu wadataccen lokaci da za ta magance matsalolinsu amma ta gagara taɓuka komai.

Har ila yau shugaban kungiyar ya ce majalisar zartarwar kungiyar za ta zauna domin kara kallon lamarin.

A cewarsa majalisar zartarwar ta lura da cewa gwamnatin ta nuna halin ko in kula kan matsalolin kungiyar saboda haka dole su dauki mataki, rahoton Business Day.

Manyan bukatun kungiyar ASUU guda 9

1. Farkon abin da ASUU ta zargi gwamnatin Tinubu da shi shine rashin bada kofa domin cigaba da tattaunawa kan yarjejeniyar da suka yi da gwamnati a 2009 (2009 FGN/ASUU Agreement).

Yarjejeniyar za ta bada dama wurin samun walwala ne ga malaman jami’a domin yin aiki cikin tsari.

2. Abu na biyu shine rusa tsarin majalisun gudanar da jami’o’i da shugaba Tinubu ya yi a watan Yunin 2023.

Kungiyar ta ce rusa majalisun ya saɓa dokar kasa kuma ya haifar da giɓi babba a aikin jami’a a Najeriya.

3. Abu na gaba da kungiyar ASUU ta zargi gwamnatin a kai shine cigaba da biyan malaman jami’a albashi ta manhajar IPPIS.

Duk da cewa Bola Tinubu ya ce an cire malaman jami’o’i a tsarin tun watan Disambar bara amma kungiyar ta ce babu abin da ya canja.

4. Lamarin na hudu da zai iya jefa kungiyar yajin aiki shine fitar da sabon tsarin karatun jami’a a Najeriya.

Kungiyar ta yi watsi da sabon tsarin da gwamnati ta fitar na karatun jami’a duk da cewa gwamnatin na kokarin tilasta aiki da shi.

5. Yawaitar jami’o’in gwamnati a Najeriya shine abu na biyar da kungiyar ta koka ga gwamnatin Bola Tinubu.

Kungiyar ta ce maimakon inganta jami’o’in da ake dasu gwamantin ta dukufa wurin samar da sababbin jami’o’in da ba za ta iya daukan nauyinsu yadda ya kamata ba.

6. Abu na shida da ake dambarwa a kai shine cigaba da ɗaukan dawainiyar jami’o’i yadda ya kamata.

Kungiyar ASUU ta zargi gwamnatin tarayya da kokarin karkatar da kudaden da hukumar TETFund ke amfani da su wajen raya jami’o’i zuwa harkokin lamunin dalibai.

7. Korar ma’aikatan jami’a ba bisa ka’ida ba shine abu na bakwai da kungiyar ASUU ta ke kalubalantar gwamantin Tinubu.

Kungiyar ta ce tana da rahotanni a kan yadda ake wulakanta jami’anta a jami’ar Lagos da jami’ar Kogi da jami’ar fasaha da ke Owerri.

8. Abu na takwas da kungiyar ASUU ta koka shine yadda gwamnatin to tsohe kunnuwa kan alawus da ya kamata ta biya ta.

Gwamnatin ta gaza saka kudin alawus din da kungiyar ke binta a cikin kasafin kudin shekarar 2023.

9. A karshe kungiyar ta koka kan yadda lamura suka tabarbare a Najeriya da yadda talakawa ke kara shiga kuncin rayuwa.

A cewar kungiyar, dole gwamantin Bola Tinubu ta nemo mafita domin saukaka rayuwar al’ummar Najeriya.

Share186Tweet117SendShare
ADVERTISEMENT
Previous Post

Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf; Ya Bada Goron Sallah Ga Mahajjatan Kano

Next Post

An sami karin wadanda suka rasa rayukansu a harin masallacin k/h Gezawa

aksam

aksam

RelatedPosts

Wani Matashi Ya Rasu A Gidan Budurwarsa  ƴar Tik-tok  Dake Unguwar  Ɗanbare A Jihar Kano
LABARAI

Wani Matashi Ya Rasu A Gidan Budurwarsa ƴar Tik-tok Dake Unguwar Ɗanbare A Jihar Kano

by aksam
June 20, 2026
Gwamnatin Kano Ta Jaddada Haɗin Gwiwa Tsakanin Kafafen Yaɗa Labarai da Hukumomin Tsaro
LABARAI

Gwamnatin Kano Ta Jaddada Haɗin Gwiwa Tsakanin Kafafen Yaɗa Labarai da Hukumomin Tsaro

by Khadija Maitaya
June 19, 2026
Sky News: Yaƙin Trump da Iran Na Daya Daga Cikin Manyan Kurakuran Dabarun Amurka
LABARAI

Sky News: Yaƙin Trump da Iran Na Daya Daga Cikin Manyan Kurakuran Dabarun Amurka

by Khadija Maitaya
June 16, 2026
China Ta Soke Darussa 12,000 na Jami’o’i Domin Shirin Zamani na AI
LABARAI

China Ta Soke Darussa 12,000 na Jami’o’i Domin Shirin Zamani na AI

by Khadija Maitaya
June 14, 2026

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Recommended.

Bayan Gaza biyan Miliyan 248 KEDCO ta yanke wutar lantarkin Jami’ar Aliko Dangote

Bayan Gaza biyan Miliyan 248 KEDCO ta yanke wutar lantarkin Jami’ar Aliko Dangote

July 1, 2024
Rudunar ‘Yan Sandan Najeriya Ta Yi Nasarar  Kama Wasu  ‘Yan Ta’adda   Su  Biyar Da Take Zargin Kwararone  Wajan Yin Garkuwa Da Mutane;  A Yankin Arewa Masu Yamma

Rudunar ‘Yan Sandan Najeriya Ta Yi Nasarar Kama Wasu ‘Yan Ta’adda Su Biyar Da Take Zargin Kwararone Wajan Yin Garkuwa Da Mutane; A Yankin Arewa Masu Yamma

February 16, 2024
ADVERTISEMENT

Trending.

Mu Na Gayyatar  ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Gurin Daurin Auren:- Ango Bulaye

Mu Na Gayyatar ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Gurin Daurin Auren:- Ango Bulaye

June 12, 2026
An Kammala Gasar Kwallon Kafar Sada Zumunchi Dan Muna Murnar Zagayuwar Sallah Babba Cikin Nasara A Garin Nkawkawo Dake Kasar Ghana

An Kammala Gasar Kwallon Kafar Sada Zumunchi Dan Muna Murnar Zagayuwar Sallah Babba Cikin Nasara A Garin Nkawkawo Dake Kasar Ghana

June 1, 2026
The Emir of Zangon Nkawkawo, Alhaji Abdul-Nasir Usman, Extends Eid Greetings

The Emir of Zangon Nkawkawo, Alhaji Abdul-Nasir Usman, Extends Eid Greetings

June 1, 2026
Irin Yadda Ake Cigaba Da Gudanar Da  Karatun Saukar Al’qur’ani Mai Girma  A Zango Nkawkawo Dake Kasar Ghana

Irin Yadda Ake Cigaba Da Gudanar Da Karatun Saukar Al’qur’ani Mai Girma A Zango Nkawkawo Dake Kasar Ghana

June 5, 2026
Ga Sakon Bangajiya Daga: Angon Sha’ibu Sani Mai Atamfa (Bulaye)

Ga Sakon Bangajiya Daga: Angon Sha’ibu Sani Mai Atamfa (Bulaye)

June 15, 2026

Aksam Hausa

AKSAM MEDIA is a company which designed as online News Platform and other activities related to develop society.

The AKSAM MEDIA created since November 2019 and it does many activities as News publishes it publishes a Hausa News And English News.

No Result
View All Result
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO

© 2023 Aksam media