• About
  • Advertise
  • Privacy & Policy
  • Contact
AKSAM
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO
No Result
View All Result
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO
No Result
View All Result
AKSAM
No Result
View All Result

Gwamnatin Shugaba Bola Tinubu Ta Yi Wa Gwamnonin PDP Martani Akan Matsalar Tattalin Arziki

aksam by aksam
February 15, 2024
Reading Time: 2 mins read
0
Home SIYASA
ADVERTISEMENT
467
SHARES
1.5k
VIEWS
Share on FacebookShare on Twitter

DAGA HASSAN UMAR GWAMMAJA

Bayan sun kwatanta halin da tattalin arzikin Najeriya ya ke ciki da irin na ƙasar Venezuela.

RelatedPosts

Tsohon Gwamnan Jihar Kano, Rabiu Musa Kwankwaso, Ya Koma Jam’iyyar National Democratic Congress (NDC) A Hukumance; Inda Ya Karɓi Katin Zama Mamba Na Jam’iyyar

Gwamnan Jihar Bauchi, Sanata Bala Mohammed Ya Fice Daga Jam’iyar PDP

Wasu Dalilin Da Suka Sa Kwankwaso Ke Shirin Ficewa Daga Jam’iyyar ADC

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Mohammed Idris ya ce duk da dai tattalin arzikin Najeriya na fuskantar ƙalubale, kwatanta shi kafaɗa-da-kafaɗa da na Venezuela da gwamnonin PDP suka yi, rashin adalci ne ainun.

“Muna bayyana cewa duk da ƙasar mu na fuskantar wasu matsaloli, waɗanda kuma wannan gwamnati ta Shugaba Bola Tinubu na ƙoƙarin magance su, to kuma matsalolin mu ko kusa ba su kai ga na Venezuela ba, kamar yadda gwamnonin PDP suka rufe ido suka faɗa,” haka Idris ya bayyana a cikin wata sanarwar da aka raba wa PREMIUM TIMES a ranar Talata.

“Tattalin arzikin Najeriya har yanzu ya na da ƙarfi sosai, kuma ana sa rai da kyakkyawan hasashen cewa zai bunƙasa da ƙarin kashi 3% bisa 100% cikin wannan shekarar.

“Tattalin arzikin mu na bayar da gudunmawar lamuni ga masu ramce a cikin gida da waje.”

A ranar Litinin ce dai gwamnonin PDP suka gudanar da taro a Abuja, inda suka tattauna batutuwa, musamman waɗanda suka shafi matsalar tsaro da matsalar tattalin arziki, wadda ta haifar da matsalar tsada da raɗaɗin tsadar rayuwa.

Bayan kammala taron, sun bada sanarwar cewa sun amince kowace jiha a ba ta damar kafa ‘yan sandan jiha, domin a samu a shawo kan ƙalubalen matsalar tsaro a faɗin ƙasar.

Minista Idris ya ce muna maraba da shawarwarin da suka bayar waɗanda ba na son rai ba, domin ganin an magance matsalolin tsaro da na tattalin arziki,” inji Idris.

Daga nan kuma ya fara ragargazar gwamnonin da cewa sun taimaka wajen haifar da matsalar tattalin arziki.

“A matsayin su na shugabanni a gwamnatocin jihohi, gwammonin PDP su na da ‘yancin bayyana matsayar su kan duk wani abu da ya shafi ƙasar nan.

“ ya kamata a ce masu shiga sahun gaban inganta tattalin arziki ne, samar da yalwa a ƙasa ga ‘yan ƙasar a jihohin su, a ce kuma sun koma su na furka kalaman ƙage da shaci-faɗi kan Najeriya, har su na kwatanta matsalar tattalin arzikin Najeriya da irin matsalolin da suka dabaibaye tattalin arzikin Venezuela.

“Mu na son mu bayyana cewa duk da dai tattalin arzikin mu na fuskantar ƙalubale, amma ki kusa ba daidai ba ne a kwatanta matsalar Venezuela da ta Najeriya.

“Ya yin da gwamnatin tarayya ke biyan albashi da sauran haƙƙoƙin ma’aikata kan kari, kuma harkokin gwamnati na tafiya dai-dai-wa-dai-da, ya kamata ‘yan Najeriya su tambayi gwamnonin PDP abin da suka yi da kuɗaɗen da ake ba su. Saboda akwai rahoton bincike mai nuna cewa yawancin jihohin PDP sun kasa biyan ‘yan fansho kuɗaɗen su na tsawon watanni da dama, haka albashin ma’aikata ma wasu ba su biya yadda ya kamata. Gwamnonin PDP na ƙin biyan garatutin ma’aikatan da suka yi ritaya.

“Haka kuma wasu gwamnonin PDP ɗin har yau sun kasa ma biyan Naira 30,000 a matsayin mafi ƙarancin albashi, shekaru huɗu da gwamnatin tarayya ta fara amfani da tsarin,” inji Minista Idris.

Share187Tweet117SendShare
ADVERTISEMENT
Previous Post

Kungiyar Masu Gidajen Bride A Najeriya Zasu Fara Yajin Aiki

Next Post

Shahararren Dan Wasan Kwallon Kafa Dake Buga Wasa A Kungiyar Kwallon Kafa Ta Al Nassr, Cristiano Ronaldo Ya Buga Wasannin Dubu (1000) A Tarihi

aksam

aksam

RelatedPosts

Tsohon Gwamnan Jihar Kano, Rabiu Musa Kwankwaso, Ya Koma  Jam’iyyar National Democratic Congress (NDC)  A Hukumance; Inda Ya Karɓi Katin Zama Mamba Na Jam’iyyar
SIYASA

Tsohon Gwamnan Jihar Kano, Rabiu Musa Kwankwaso, Ya Koma Jam’iyyar National Democratic Congress (NDC) A Hukumance; Inda Ya Karɓi Katin Zama Mamba Na Jam’iyyar

by aksam
May 3, 2026
Gwamnatin Jihar Bauchi Ta Umarci  Duk Masu Riƙe Da Mukaman Siyasa Dake Da Niyyar Tsayawa Takara Dasu Yi Murabus Kafin Ranar Juma’a 24 ga Watan Afrilu 2026
SIYASA

Gwamnan Jihar Bauchi, Sanata Bala Mohammed Ya Fice Daga Jam’iyar PDP

by aksam
May 2, 2026
Ba Za Mu Bawa Kwankwaso Tikitin Takarar Shugabancin Kasa A Jam’iyyarmu— NNPP
SIYASA

Wasu Dalilin Da Suka Sa Kwankwaso Ke Shirin Ficewa Daga Jam’iyyar ADC

by aksam
May 2, 2026
Masu Ruwa Da Tsaki A  APCn Kano Sun Amince Da Takarar Abba da Tinubu Karo Na Biyu A Zaɓen 2027
SIYASA

Masu Ruwa Da Tsaki A APCn Kano Sun Amince Da Takarar Abba da Tinubu Karo Na Biyu A Zaɓen 2027

by aksam
May 1, 2026

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Recommended.

Gwamna Abba Kabir ya mayar wa Ogan Boye mukaminsa tare da nada wasu mutane 8

Gwamna Abba Kabir ya mayar wa Ogan Boye mukaminsa tare da nada wasu mutane 8

April 9, 2024
Gwamnatin Tarayya Ta Fitar da sabon jerin sunayen Masu ɗaukar nauyin taaddanci ya haɗa da Tukur Mamu, Simon Ekpa Da Wasu 46

Gwamnatin Tarayya Ta Fitar da sabon jerin sunayen Masu ɗaukar nauyin taaddanci ya haɗa da Tukur Mamu, Simon Ekpa Da Wasu 46

April 12, 2026
ADVERTISEMENT

Trending.

Mu Na Gayyatar  ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Gurin Daurin Auren:- Comr.  Usaini Sani Adamu !!!

Mu Na Gayyatar ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Gurin Daurin Auren:- Comr. Usaini Sani Adamu !!!

April 24, 2026
Ga Sakon Bangajiya Daga: Angon Umar SA’ID

Ga Sakon Bangajiya Daga: Angon Umar SA’ID

April 20, 2026
Shekara Kwana: Shekaru 24 Kenan Da Hatsarin Jirgin Sama A Unguwar Gwammaja Dake Jihar Kano

Shekara Kwana: Shekaru 24 Kenan Da Hatsarin Jirgin Sama A Unguwar Gwammaja Dake Jihar Kano

May 4, 2026
Muna Gayyatar ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Daurin Auren;- UMAR SA’ID

Muna Gayyatar ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Daurin Auren;- UMAR SA’ID

April 17, 2026
Atiku, Kwankwaso , Obi Sun Jagoranci Zanga-Zanga A Babban Birnin Tarayya Abuja

Atiku, Kwankwaso , Obi Sun Jagoranci Zanga-Zanga A Babban Birnin Tarayya Abuja

April 8, 2026

Aksam Hausa

AKSAM MEDIA is a company which designed as online News Platform and other activities related to develop society.

The AKSAM MEDIA created since November 2019 and it does many activities as News publishes it publishes a Hausa News And English News.

No Result
View All Result
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO

© 2023 Aksam media