DAGA HASSAN UMAR GWAMMAJA
Daruruwan dalibai ne suka yi dandazo a Kano a yau Litinin don nuna adawa da yadda ake ci gaba da yin garkuwa da dalibai mata a manyan makarantun Arewacin Najeriya.
Daliban da suka yi tattaki a unguwar Rijiyar Zaki da ke cikin birnin Kano, sun bukaci a gaggauta ceto dalibai mata da wasu ‘yan bindiga dauke da makamai suka yi garkuwa da su a Jami’ar Tarayya ta Gusau wato FUGUS kimanin watanni uku da suka gabata, da kuma wasu da aka yi garkuwa da su a Jami’ar Tarayya da ke Dutsin-ma,a jihar Katsina wato FUDMA da sauransur na Jami’ar Jihar Nasarawa dake Keffi.
Kimanin dalibai mata 24 na FUGUS, da kuma dalibai mata hudu na FUDMA da ‘yan bindiga suka kama sama da watanni uku da suka gabata, har yanzu suna hannunsu kamar yanda Jaridar Daily Post ta ruwaito
Sai dai a ranar Lahadin da ta gabata an sako wasu dalibai bakwai na Jami’ar Tarayya da ke Lafia, FULAFIA, Jihar Nasarawa, wadanda ‘yan bindiga suka yi garkuwa da su kwanaki hudu da suka gabata.
Amma har yanzu dalibai hudu da aka kama daga jami’ar jihar Nasarawa watannin baya suna hannunsu.
An gudanar da zanga-zangar ne a karkashin tutar ‘Arewa Mufarka’ ma’ana ‘Yan Arewa mu farka.
Da yake zantawa da manema labarai jagoran zanga-zangar Sharfuddeen Bature, ya ce: “Mun dade muna kan lamarin. Yau kwana tamanin kenan da sace mutanen. Muna da ministocin tsaro a yankinmu jihar Jigawa da jihar Zamfara. Muna da mai ba da shawara kan harkokin tsaro, NSA, daga yankin mu (Jihar Adamawa).
“Muna bukatar dawowar wadannan ‘yan matan. Iyayen su suna cikin mawuyacin hali. Ba za mu daina yin haka ba har sai sun dawo da ‘yan matanmu”.
Masu zanga-zangar sun kuma yi Allah wadai da kisan kiyashin da jiragen yakin sojin Najeriya suka yi a baya-bayan nan sama da mutane 127 a kauyin Tudun Biri da ke karamar hukumar Igabi a jihar Kaduna.










