• About
  • Advertise
  • Privacy & Policy
  • Contact
AKSAM
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO
No Result
View All Result
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO
No Result
View All Result
AKSAM
No Result
View All Result

Karuwar Yawan Satar Dalibai A Jami’o’in Najeriya; ‘Yan Arewa Sun Gudanar Da Zanga-Zangar Lumana

aksam by aksam
December 11, 2023
Reading Time: 2 mins read
0
Home TSARO
ADVERTISEMENT
470
SHARES
1.5k
VIEWS
Share on FacebookShare on Twitter

DAGA HASSAN UMAR GWAMMAJA

Daruruwan dalibai ne suka yi dandazo a Kano a yau Litinin don nuna adawa da yadda ake ci gaba da yin garkuwa da dalibai mata a manyan makarantun Arewacin Najeriya.

RelatedPosts

Rundunar Sojin Najeriya ta ayyana neman jami’inta ruwa a jallo

Peace Corps of Nigeria Ta Yi Bikin Cika Shekaru 28 da Kafuwa

Jerin kamfanin tsaro na Amurka 10 da ‎China Ta Kakaba wa Takunkumi

Daliban da suka yi tattaki a unguwar Rijiyar Zaki da ke cikin birnin Kano, sun bukaci a gaggauta ceto dalibai mata da wasu ‘yan bindiga dauke da makamai suka yi garkuwa da su a Jami’ar Tarayya ta Gusau wato FUGUS kimanin watanni uku da suka gabata, da kuma wasu da aka yi garkuwa da su a Jami’ar Tarayya da ke Dutsin-ma,a jihar Katsina wato FUDMA da sauransur na Jami’ar Jihar Nasarawa dake Keffi.

Kimanin dalibai mata 24 na FUGUS, da kuma dalibai mata hudu na FUDMA da ‘yan bindiga suka kama sama da watanni uku da suka gabata, har yanzu suna hannunsu kamar yanda Jaridar Daily Post ta ruwaito

Sai dai a ranar Lahadin da ta gabata an sako wasu dalibai bakwai na Jami’ar Tarayya da ke Lafia, FULAFIA, Jihar Nasarawa, wadanda ‘yan bindiga suka yi garkuwa da su kwanaki hudu da suka gabata.

Amma har yanzu dalibai hudu da aka kama daga jami’ar jihar Nasarawa watannin baya suna hannunsu.

An gudanar da zanga-zangar ne a karkashin tutar ‘Arewa Mufarka’ ma’ana ‘Yan Arewa mu farka.

Da yake zantawa da manema labarai jagoran zanga-zangar Sharfuddeen Bature, ya ce: “Mun dade muna kan lamarin. Yau kwana tamanin kenan da sace mutanen. Muna da ministocin tsaro a yankinmu jihar Jigawa da jihar Zamfara. Muna da mai ba da shawara kan harkokin tsaro, NSA, daga yankin mu (Jihar Adamawa).

“Muna bukatar dawowar wadannan ‘yan matan. Iyayen su suna cikin mawuyacin hali. Ba za mu daina yin haka ba har sai sun dawo da ‘yan matanmu”.

Masu zanga-zangar sun kuma yi Allah wadai da kisan kiyashin da jiragen yakin sojin Najeriya suka yi a baya-bayan nan sama da mutane 127 a kauyin Tudun Biri da ke karamar hukumar Igabi a jihar Kaduna.

Share188Tweet118SendShare
ADVERTISEMENT
Previous Post

Hukumar EFCC Na Tuhumar Wasu Ma’aurata Da Aikata Damfarar; Naira Miliyan 410.5

Next Post

Zamu ci gaba da bibiya har sai an yi adalci ga mutanen da harin bomb ya rutsa da su a Tudun Biri: Sarkin Musulmai

aksam

aksam

RelatedPosts

Rundunar Sojin Najeriya ta ayyana neman jami’inta ruwa a jallo
TSARO

Rundunar Sojin Najeriya ta ayyana neman jami’inta ruwa a jallo

by Khadija Maitaya
July 24, 2026
Peace Corps of Nigeria Ta Yi Bikin Cika Shekaru 28 da Kafuwa
LABARAI

Peace Corps of Nigeria Ta Yi Bikin Cika Shekaru 28 da Kafuwa

by Khadija Maitaya
July 10, 2026
Sky News: Yaƙin Trump da Iran Na Daya Daga Cikin Manyan Kurakuran Dabarun Amurka
LABARAI

Jerin kamfanin tsaro na Amurka 10 da ‎China Ta Kakaba wa Takunkumi

by Khadija Maitaya
June 22, 2026
Rundunar  Sojin Najeriya Ta Yi Nasarar Ceto Matar Marigayi Janar Rabe Abubakar Daga Hannun Masu Garkuwa Da Mutane
TSARO

Rundunar Sojin Najeriya Ta Yi Nasarar Ceto Matar Marigayi Janar Rabe Abubakar Daga Hannun Masu Garkuwa Da Mutane

by aksam
June 16, 2026

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Recommended.

Alhaji Yusuf Umar Kirgi Dake Mazabar Haskiya, K/Hukumar Kubau; Yana Gayyatar Uwa Da Abokanan Arziki, Daurin Auren Dan Sa

Alhaji Yusuf Umar Kirgi Dake Mazabar Haskiya, K/Hukumar Kubau; Yana Gayyatar Uwa Da Abokanan Arziki, Daurin Auren Dan Sa

December 8, 2023
Aliko Dangote Ya Kafa Tarihi: Ya Zama Dan Afrika Na Farko Da Ya Kai Dukiya Har Dala Biliyan 30

Aliko Dangote Ya Kafa Tarihi: Ya Zama Dan Afrika Na Farko Da Ya Kai Dukiya Har Dala Biliyan 30

October 24, 2025
ADVERTISEMENT

Trending.

Masu Siye Da Siyar Da Filaye A  R/zakara Sunkoka Da Aibantasu Da Gwamnatin Kano Keyi.

Masu Siye Da Siyar Da Filaye A  R/zakara Sunkoka Da Aibantasu Da Gwamnatin Kano Keyi.

August 26, 2026
Cristiano Ronaldo Ya Auri Georgina Rodríguez

Cristiano Ronaldo Ya Auri Georgina Rodríguez

August 12, 2026
Wani Kauran Mata Ya Jikkata Wata Dattijuwa Bayan Ta Hana Shi Shiga Gurin Da Bai kamata Ba

Wani Kauran Mata Ya Jikkata Wata Dattijuwa Bayan Ta Hana Shi Shiga Gurin Da Bai kamata Ba

August 29, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Matar Aure Hukunci Bayan Samunta Da Watsa Tafasasshen Ruwa Ga Kishiyarta

Kotu Ta Yanke Wa Matar Aure Hukunci Bayan Samunta Da Watsa Tafasasshen Ruwa Ga Kishiyarta

August 7, 2026
Iran Ta Kakkabo Wasu Manyan Jiragen Yaƙi Na Amurka

Iran Ta Kakkabo Wasu Manyan Jiragen Yaƙi Na Amurka

August 14, 2026

Aksam Hausa

AKSAM MEDIA is a company which designed as online News Platform and other activities related to develop society.

The AKSAM MEDIA created since November 2019 and it does many activities as News publishes it publishes a Hausa News And English News.

No Result
View All Result
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO

© 2023 Aksam media