Ya ce,”Mun amince a binciki yadda wannan hari ya faru, domin ni a iya sanina irin wannan kuskuren kai wa mutanen da ba su ji ba su gani ba hari da sojojin Najeriya suka yi ya kai 16.
“A jihata Borno, an sha samun irin wannan harin,” in ji shi.
Sanata Ali Ndume, ya ƙara da cewa irin wadannan hare hare sun zamo abin damuwa domin ba sau daya aka taba samun irin haka ta faru ba, kuma mutanen da aka kashe a irin wadannan hare haren kuskuren jimillarsu ya kusa kai wa 500, a cewarsa.
“Don haka bai kamata a ci gaba da kai irin wadannan hare hare ba, saboda jami’an tsaro an san aikinsu shi ne tabbatar da tsaro da kare rayukan al’umma, amma kuma su zo suna kai irin wadannan hari, zai zama ke nan kwalliya ba ta biya kudin sabulu ba aikin da suke ke nan.”
Ndume ya ce, “ Ina tabbatar da cewa mu ‘yan majalisa za mu yi iya bakin kokarinmu don ganin an binciki wannan lamari da kuma tsayar da shi saboda gaba.”
Ya ce binciken da ya kamata a yi tare da bayar da shawarar ɗauko masu bincike masu zaman kansu kuma kwararru su gudanar da bincike a kan harin, sannan a yi binciken da wuri kuma a gani a kasa.












