Hukumar hisbah ta jihar Kano ta yabawa kungiyar mata musulmi sufaye bisa jajircewar ta akan harkokin ci gaban al’umma a jihar kano.mataimakiyar kwamandan hukumar a bangaren mata
Malama Khadija sagir sulaiman ce ta bayyana hakan Yayin kaddamar da kungiyar tare da mauludin Sidi Abdulkadir jilani R T A da Kuma cikar malama Baraka shekara goma akan kujerar Naqibatul kadiriyya .
Dr Khadija ta ce fatan hukumar kungiyoyi su kasance manyan ayyukansu sune hidimtawa addini domin babu dacen da yakai haka don haka ta ja hankalin kungiyar mata musulmi sufayen da su kaucewa sa son zuciya ko meman biyan bukatu na kashin kansu ba tare da sun fifita harkar musulmci a sahun gaba ba
Ita ma malama Baraka Adamu Danfanta ta nuna Jin dadinta game da kaddamar da kungiyar tare da kasancewar ta a matsayin Naqibatul kadiriyya a jihar Kano
Naqibatul kadiriyyar ta kuma yi fatan dukkan addu’o’in da akayi a wannan wuri su zama karbabbu.Taron ya samu halattar manyan baki kamar jigo a jam’iyyar NNPP Wanda ya wakilci gwamna Honorabil Sunusi Surajo kwankwaso da Kuma Galadiman gado da masun Kano Alhaji Dayyab Ahmad Mai turare da sauransu wakiliyarmu jamila sulaiman Aliyu ta labarta Mana cewa an gudanar da addu’o’in samu sassauci a rayuwar musulmin duniya ga baki daya.












