Malaman addinin Musulunci a Najeriya sun isar da koken talakawa ga shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu a fadar Aso Villa ranar Alhamis
Bayan ganawa da Tinubu, malaman sun roƙi ƴan Najeriya musamman matasa su haƙura sun janye zanga-zangar da suke shirin yi a watan Agusta
Shugaban Izala kuma jagoran tawagar malaman da suka gana da Tinubu, Abdullahi Bala Lau ya roƙi Musulmi da Kirista su taya Tinubu da addu’a











